- Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin Sanata David Mark ta sake jaddada kudurinta na tsayawa takarar zaɓen shekarar 2027 a karkashin tutarta, duk da cece-kuce da ake yi kan matsayar Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) game da shugabancin jam’iyyar bayan umarnin kotu.
Da yake magana a shirin Politics Today na tashar Channels Television a ranar Talata, Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya bayyana cikakken kwarin gwiwa ga bangaren shari’a tare da shirye-shiryen jam’iyyar na fuskantar duk wata ƙalubale ta siyasa da doka.
“Abu guda da zan iya tabbatarwa shi ne za mu shiga zaɓen 2027 a karkashin ADC,” in ji Abdullahi.
Ya ƙara da cewa jam’iyyar na da tabbacin cewa za ta yi nasara a kotu, inda ya bayyana shari’ar su a matsayin mai ƙarfi sosai.
“Duk da abubuwan da suka faru a Najeriya, har yanzu muna da cikakken yarda da bangaren shari’a. Mun yi imanin cewa shari’ar mu mai sauƙin cin nasara ce (slam-dunk). Idan aka ba mu damar sauraron gaggawa, muna da yakinin za a yi adalci.”
Abdullahi ya kuma bayyana cewa jam’iyyar ta bi dukkan ka’idojin da doka ta tanada, ciki har da sanar da INEC kafin gudanar da tarurrukan ta.
Ya ce sauyin matsayar INEC ba zai hana su cimma burinsu ba.
“Idan INEC ɗin da ta rantse a kotu cewa tana sane da sauyin shugabanci a ADC yanzu ta sauya magana, hakan ba zai hana mu ba.”
Jam’iyyar ta kuma bayyana cewa tana shirye don fuskantar duk wani sakamako, yayin da take fatan samun nasara a kotu.
Add A Comment
