Jam’iyyar LP ta yi watsi da kalaman tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar shekarar 2023, Peter Obi, wanda a kwanakin nan ya buƙaci magoya bayansa da su zaɓi ‘yan takarar jam’iyyar haɗaka ta ADC a zaɓen cike gurbi da ake shirin yi.
Za a yi zaɓukan cike gurbin ne a ranar 16 ga watan Agusta, inda jam’iyyar LP ta ayyana matakin Obi da “yaudara da mafarkin da ba zai taɓa zama gaskiya.”
Wannan dai na ƙunshe ne cikin wani jawabi da shugaban jam’iyyar LP na ƙasa, Julius Abure, wanda lauya ne, ya wallafa a shafin jam’iyyar na X.
“An ja hankalin shugabancin jam’iyyar Labour Party kna kalaman da to tsohon ɗan takararmu a zaɓen shugaba ƙasa Peter Obi, ya yi, inda ya ba wa ‘yan jam’iyyar umarnin zaɓen wata jam’iyyar a zaɓen cike gurbi da za a yi a ranar 16 ga watan Agusta.”
“Abin takaici ne yadda Obi ya maishe da kansa abin shaguɓe a fagen siyasar Najeriya.
Ya maishe da kansa kamar “ɗan karen farauta” wanda ba ya iya tsayawa kan ra’ayin kansa,” a cewar sanarwar.
“A yanzu yana ƙoƙarin sanya kansa cikin kundin abubuwan al’ajabi na (Guinness book of records) a matsayin wanda ya fi kowa tsare-tsaren shiga jam’iyyun siyasa duk domin samun mulkin Najeriya.”
Sanarwar ta ce, Peter Obi ne silar rikicin da ke faruwa a jam’iyyar a yayin da yake amfani da hakan wajen kafa dalilin cewa ka da a zaɓi jam’iyyar saboda rikice-rikice
LP ta buga misali da lokacin da Peter Obi da Alex Otti, gwamnan Abia duka shirya wani haramtaccen taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a ranar 4 ga watan Satumbar 2024.
“Yana daga cikin waɗanda suka haifar da rikicin a tsawon wannan lokaci, a yayin da ta kai ya jagoranci zanga-zanga zuwa shalkwatar INEC don nuna adawa da jam’iyyarsa,” in ji Abure.
“Fafutukar karɓe iko da jam’iyyar ya sa shi shiga daji.”
Abure ya ce wannan jam’iyya ce da ta yi masa sha tara ta arziki, amma sai ga shi ya saka mata da mugunta.
“Wannan ce ta sa muke cewa Obi bai da cancanta da kamala da kafasiti da zai iya samar da sabuwar Najeriya.”
“Abin da Obi bai sani ba shi ne jam’iyyarmu tana sahun jam’iyyu a takardar kaɗa kuri’a kuma ‘yan takarkarunmu sun shiga zaɓe, duk kuwa da ƙoƙarin murɗe wa jam’iyyar wuya da ya yi,” shugaban jam’iyyar ya bayyana.
Daga nan jam’iyyar ta yi kira ga dukkan ‘ya’yanta da ‘yan takarkarunmu da magoya bayanta da ke ko’ina a Najeriya da su fito zaɓen cike gurbi da tabbatar da sun yi zaɓe.
“‘Yan Najeriya yanzu sun san wane ne Peter Obi a zahiri,” in ji Abure a jawabin da ya fitar.