
akwai aikin sabunta sashin Mata da kananan Yara da ta ke gudanarwa a Asibitin, a domin haka take sanar da mutane cewar ayyuka za su ragu a bangaren.
Hakan na cikin wata sanarwa da jami’ar Yada labarai ta ma’aikatar Hajiya Samira Sulaiman ta fitar.
Sanarwar ta kuma bukaci al’umma da su ziyarci wasu Asibitocin gwamnati dake jihar a lokacin da ake gudanar da aikin.
Kazalika sanarwar ta kara baiwa al’umma hakuri kan tsaikon da aka samu da cewa yana daga cikin kidirin gwamnatin Kano na kara inganta fannin Lafiya wanda hakan ne yasa take gudanar da aikin.