Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    Najeriya Ta Kai Dala $18.4 Biliyan a Cinikayyar Cikin Afirka a 2024

    June 28, 2025

    Afreximbank Ta Ba Najeriya Tallafin $50 Biliyan Don Manyan Ayyuka

    June 28, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    Najeriya Ta Samu Jarin Waje Har Dala Biliyan 2.5 Daga Masarautar Saudiyya

    June 29, 2025

    Jihohi sun raba Naira biliyan 22.9 a matsayin kudin gyaran muhalli

    September 1, 2025

    Gwamna Bago Ya Rusa Majalisar Ministocinsa a Neja

    September 1, 2025

    Atiku Ya Bukaci Jam’iyyun Adawa Su Ƙi Karɓar Sakamakon Zaɓen Rivers

    September 1, 2025

    Tinubu ya na adalci ga kowanne yanki na ƙasar nan – Ministan Yaɗa Labarai

    September 1, 2025
  • Asrah 24 TV
  • Education

    CP FCT Ya Ziyarci CBT Centres, Ya Tabbatar da Tsaro Yayin JAMB UTME

    April 16, 2026

    Fiye da miliyan 2.2 za su rubuta UTME 2026 a fadin Najeriya

    April 16, 2026

    An Gargadi Dalibai su Gina Hali da Jagoranci a LAPO Institute

    April 15, 2026

    Gwamnatin Katsina ta horas da ma’aurata 1,000 kafin bikin ‘Auren Gata’

    April 9, 2026

    Ƴar Najeriya ta lashe gasar iya Turanci ta duniya a London

    August 5, 2025
  • Health

    Ka guji sayen kayayyakin da ba su da lakabi ko rajista – CPC Imo ta yi gargadi

    April 15, 2026

    Likita ya danganta yawaitar cutar koda da rashin shan ruwa da yawan amfani da maganin ciwo

    April 15, 2026

    NARD ta goyi bayan yajin aiki na sa’o’i 48 a Delta kan dukan likitoci

    April 13, 2026

    Shugaban Karamar Hukumar Kosofe Ya Fallasa Shago da Salon Gashi a Cikin Bandaki a Kasuwar Lagos

    April 11, 2026

    Gwamnatin Abia da Likitocin Amurka Za Su Gudanar da Aikin Jinya Kyauta

    April 11, 2026
  • Podcast
  • Politics

    CAC Ta Tabbatar da Kutse a Tsarin Kwamfuta, Ta Fara Bincike Kan Tsaro

    April 16, 2026

    Democrat Sun Kaddamar da Yunkurin Tsige Shugaban Pentagon, Hegseth

    April 16, 2026

    Nasarawa Gov Faults Leaders for Calling Salaries, Roads Achievements

    April 16, 2026

    Fadar Shugaban Kasa ta ce Kudancin Najeriya ya kammala rabon mulki kafin 2027

    April 16, 2026

    Gwamnan Ogun ya amince da hutun rana guda a mako, da ₦10,000 kudin sufuri ga ma’aikata

    April 16, 2026
  • Sports

    NFF: Dr. Terry Eguaoje Ya Samu Sabon Lasisin Koyar da Koci daga Amurka

    April 16, 2026

    Tsohon Mai Tsaron Raga na Arsenal, Alex Manninger, Ya Rasu a Hatsarin Mota

    April 16, 2026

    Inter Miami ta Nada Guillermo Hoyos Sabon Koci

    April 16, 2026

    Inter Miami ta Nada Guillermo Hoyos Sabon Koci

    April 16, 2026

    Mikel Obi Ya Caccaki Barcelona Kan Fitar Su Daga Champions League

    April 16, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Gwamnatin Neja ta nemi sulhu da gidan rediyon Badeggi FM
News

Gwamnatin Neja ta nemi sulhu da gidan rediyon Badeggi FM

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaAugust 13, 20253 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp

IMG 2938Gwamnatin jihar Neja ta amince da sulhun bayan fage a maimakon shiga kotu da gidan rediyon Badeggi (90.1 FM Radio Station) – kafar yaɗa labarai mai zaman kansa da ke garin Minna – wanda gwamnan jihar Neja, Mohammed Bago, ya ba da umarnin rufewa.

Kafar yaɗa labaran ta shigar da gwamnatin jihar ƙara a gaban kotu kwanaki biyar bayan tilasta mata rufe gidan rediyon a ranar 5 ga Agusta ta hannun lauyanta mai suna, Philip Emmanuel.

A ranar Litinin, a lokacin zaman kotu kan shari’a mai lamba NSHCM/0296/2025 a gaban babbar kotun Minna mai lamba 4, inda lauyan gwamnati Jacob Usman ya sanar da cewa gwamnati tana son tattaunawa a wajen kotu domin sulhuntawa da gidan rediyon.

Usman ya bayyana wa kotun cewa ya tattauna da lauyan waɗanda suka shigar da ƙara domin warware matsalar saboda samun zaman lafiya albarkacin al’ummar jihar Neja.

Ya kuma bayyana wa kotun cewa ya riga ya sanar da mista Emmanuel cewa babban antoni-janar na jihar Neja ya amince ya warware matsalar a wajen kotu.

Mista Emmanuel daga baya ya tabbatar wa da ‘yan jarida cewa, “mun zaɓi ranar 3 ga Satumbar 2025 domin tattaunawa a wajen kotun.”

Mai shari’a, Mohammed Mohammed, a ranar 5 ga Agusta, ya amince da roƙon da mai shigar da ƙara gidan rediyon Badeggi Broadcasting Service Ltd, da manajin-daraktan Mohammed Badeggi.

A cikin hukuncin da ya yanke, mai shari’a Mohammed, ya dakatar da gwamnan jihar da antoni-janar da hukumar bunƙasa birane ta jihar daga ɗaukar mummunan mataki da ka iya shafar lasisin gidan rediyon da ginin gidan yaɗa labaran da ke harabar gidan NTA da ke saman dutsen Minna.

PREMIUM TIMES ta rawaito yadda gwamna Bago ya ba da umarnin rufe gidan rediyon Badeggi FM saboda zargin ƙoƙarin haifar da husuma.

Gwamnan ya ba da umarnin ne a lokacin zaman jiga-jigan jam’iyyar APC wanda aka yi a gidan gwamnati da ke Minna.

Ya kuma ce an ɗauki matakin ne saboda irin ayyukan da gidan rediyon ke yi wanda ya saɓa wa ƙa’ida.

Bago ya kuma zargi mamallakin gidan rediyon da ƙoƙarin tunzura al’umma a kan gwamnati inda ya buƙaci a soke lasisin gidan rediyon.

Gwamnan ya kuma ba wa kwamishinan tsaron cikin gida da rundunar ‘yan sanda umarnin rufe gidan rediyon.

Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama kamar SERAP da CJID sun yi Alla-wadai da matakin da gwamnan jihar ya ɗauka. Ƙungiyoyin sun kuma zargi gwamnan da ƙoƙarin murƙushe kafafen yaɗa labarai da tauye ‘yancin faɗar albarkacin baki a jihar.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleEFCC ta ba da belin tsohon gwamnan Sokoto Waziri Tambuwal da ta tsare
Next Article Gwamnatin Najeriya ta yi maraba da naɗin Maryam Bukar-Hassan a matsayin jakadiyar zaman lafiya ta duniya

Related Posts

Jihohi sun raba Naira biliyan 22.9 a matsayin kudin gyaran muhalli

September 1, 2025

Gwamna Bago Ya Rusa Majalisar Ministocinsa a Neja

September 1, 2025

Atiku Ya Bukaci Jam’iyyun Adawa Su Ƙi Karɓar Sakamakon Zaɓen Rivers

September 1, 2025

Tinubu ya na adalci ga kowanne yanki na ƙasar nan – Ministan Yaɗa Labarai

September 1, 2025
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Lura da Watan Zulki’ida 1447AH

April 16, 2026

NFF: Dr. Terry Eguaoje Ya Samu Sabon Lasisin Koyar da Koci daga Amurka

April 16, 2026

Ma’aikacin SEC Ya Bi Sawun Tinubu, Ya Fara Ba da Tallafin N10,000 ga Sojoji da ‘Yan Sanda

April 16, 2026

Tsohon Mai Tsaron Raga na Arsenal, Alex Manninger, Ya Rasu a Hatsarin Mota

April 16, 2026

Philanthropist Azeez Yusuf Ya Shiga Tseren Kujerar Majalisar Dokoki a Legas

April 16, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.