Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    Najeriya Ta Kai Dala $18.4 Biliyan a Cinikayyar Cikin Afirka a 2024

    June 28, 2025

    Afreximbank Ta Ba Najeriya Tallafin $50 Biliyan Don Manyan Ayyuka

    June 28, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    Najeriya Ta Samu Jarin Waje Har Dala Biliyan 2.5 Daga Masarautar Saudiyya

    June 29, 2025

    Tiwa Savage Ta Bayyana Yadda Take Rashin Kulawar Don Jazzy Da Mavin

    May 20, 2026

    NERC Da ONSA Sun Hada Kai Don Dakile Lalata Kayan Wutar Lantarki

    May 20, 2026

    Iran Ta Shirya Auren Jama’a Ga Masu Shirin Sadaukar Da Rayukansu A Yaki

    May 19, 2026

    NUJ-FCT Ta Gargadi ‘Yan Jarida Kan Yada Labaran Karya Gabanin Zabuka

    May 19, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

    June 5, 2026

    Achievers University Ta Bankado Zargin Damfarar Kudin Makaranta Ta N457.5m

    May 25, 2026

    NYSC ta shawarci iyaye su taimaka wa ‘ya’yansu da karin kudin tafiya

    May 21, 2026

    NYSC ta tsawaita wa wasu masu bautar kasa hidima a Gombe

    May 21, 2026

    Najeriya da Italiya sun hada kai domin tara dala biliyan 5 don tallafa wa ilimi

    May 21, 2026
  • Health

    OYO TA KWANTAR WA MAZAUNA HANKALI KAN CUTAR EBOLA, TA SA MA’AIKATAN LAFIYA CIKIN SHIRI

    June 4, 2026

    Likitan Ondo Sun Ƙara Matsin Lamba Kan Gwamnati, Sun Yi Barazanar Tsunduma Yajin Aiki

    May 19, 2026

    Coroner’s Court ta dakatar da shari’ar mutuwar ɗan Chimamanda Adichie har sai umarnin Attorney-General

    May 5, 2026

    Sarki Charles III Ya Yarda Cewa Ciwon Kansar Da Ke Damunsa Na Iya Hana Shi Ganin Dogon Aikin Da Ya Kafa

    April 30, 2026

    Masana lafiya sun bukaci daukar matakin gaggawa kan cutar sickle cell a Najeriya da Afirka

    April 29, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Tinubu Torchbearers Zai Taimaka Wajen Wayar Da Kai Da Tallafawa Gwamnati — APC Women Leader

    June 4, 2026

    INEC Ta Shirya Tsaf Domin Zaben Sanatan Ondo Kudu Ranar 20 ga Yuni

    June 4, 2026

    LP Ta Kammala Zaben Fidda Gwani, Ta Tsayar da ‘Yan Takara na Majalisa a Anambra

    June 4, 2026

    Peter Obi Ya Kare Adeboye, Ya Gargadi Matasa Kan Rarrabuwar Kabilanci Da Addini

    June 4, 2026

    Tsohon Firaministan Senegal Ousmane Sonko Ya Zama Kakakin Majalisa

    May 26, 2026
  • Sports

    Shaibu Ya Yabawa Super Eagles Da Adeboye Kan Nasarorin Unity Cup Da Wasan Poland

    June 4, 2026

    Super Eagles Na Da Ƙarfin Doke Kowace Ƙasa Duk Da Rashin Tikitin Gasar Kofin Duniya

    June 4, 2026

    Kai Havertz Ya Yabawa Jamus Karfin ‘Yan Hari Gaban Gasar Kofin Duniya Ta 2026

    June 4, 2026

    Marinakis Ya Yi Rikici A Athens Yayin Gasar EuroLeague

    May 25, 2026

    Spurs Sun Farfado Thunder, Wembanyama Ya Jagoranci Nasara A Wasan NBA

    May 25, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Gwamnatin Neja ta nemi sulhu da gidan rediyon Badeggi FM
News

Gwamnatin Neja ta nemi sulhu da gidan rediyon Badeggi FM

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaAugust 13, 20253 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp

IMG 2938Gwamnatin jihar Neja ta amince da sulhun bayan fage a maimakon shiga kotu da gidan rediyon Badeggi (90.1 FM Radio Station) – kafar yaɗa labarai mai zaman kansa da ke garin Minna – wanda gwamnan jihar Neja, Mohammed Bago, ya ba da umarnin rufewa.

Kafar yaɗa labaran ta shigar da gwamnatin jihar ƙara a gaban kotu kwanaki biyar bayan tilasta mata rufe gidan rediyon a ranar 5 ga Agusta ta hannun lauyanta mai suna, Philip Emmanuel.

A ranar Litinin, a lokacin zaman kotu kan shari’a mai lamba NSHCM/0296/2025 a gaban babbar kotun Minna mai lamba 4, inda lauyan gwamnati Jacob Usman ya sanar da cewa gwamnati tana son tattaunawa a wajen kotu domin sulhuntawa da gidan rediyon.

Usman ya bayyana wa kotun cewa ya tattauna da lauyan waɗanda suka shigar da ƙara domin warware matsalar saboda samun zaman lafiya albarkacin al’ummar jihar Neja.

Ya kuma bayyana wa kotun cewa ya riga ya sanar da mista Emmanuel cewa babban antoni-janar na jihar Neja ya amince ya warware matsalar a wajen kotu.

Mista Emmanuel daga baya ya tabbatar wa da ‘yan jarida cewa, “mun zaɓi ranar 3 ga Satumbar 2025 domin tattaunawa a wajen kotun.”

Mai shari’a, Mohammed Mohammed, a ranar 5 ga Agusta, ya amince da roƙon da mai shigar da ƙara gidan rediyon Badeggi Broadcasting Service Ltd, da manajin-daraktan Mohammed Badeggi.

A cikin hukuncin da ya yanke, mai shari’a Mohammed, ya dakatar da gwamnan jihar da antoni-janar da hukumar bunƙasa birane ta jihar daga ɗaukar mummunan mataki da ka iya shafar lasisin gidan rediyon da ginin gidan yaɗa labaran da ke harabar gidan NTA da ke saman dutsen Minna.

PREMIUM TIMES ta rawaito yadda gwamna Bago ya ba da umarnin rufe gidan rediyon Badeggi FM saboda zargin ƙoƙarin haifar da husuma.

Gwamnan ya ba da umarnin ne a lokacin zaman jiga-jigan jam’iyyar APC wanda aka yi a gidan gwamnati da ke Minna.

Ya kuma ce an ɗauki matakin ne saboda irin ayyukan da gidan rediyon ke yi wanda ya saɓa wa ƙa’ida.

Bago ya kuma zargi mamallakin gidan rediyon da ƙoƙarin tunzura al’umma a kan gwamnati inda ya buƙaci a soke lasisin gidan rediyon.

Gwamnan ya kuma ba wa kwamishinan tsaron cikin gida da rundunar ‘yan sanda umarnin rufe gidan rediyon.

Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama kamar SERAP da CJID sun yi Alla-wadai da matakin da gwamnan jihar ya ɗauka. Ƙungiyoyin sun kuma zargi gwamnan da ƙoƙarin murƙushe kafafen yaɗa labarai da tauye ‘yancin faɗar albarkacin baki a jihar.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleEFCC ta ba da belin tsohon gwamnan Sokoto Waziri Tambuwal da ta tsare
Next Article Gwamnatin Najeriya ta yi maraba da naɗin Maryam Bukar-Hassan a matsayin jakadiyar zaman lafiya ta duniya

Related Posts

Tiwa Savage Ta Bayyana Yadda Take Rashin Kulawar Don Jazzy Da Mavin

May 20, 2026

NERC Da ONSA Sun Hada Kai Don Dakile Lalata Kayan Wutar Lantarki

May 20, 2026

Iran Ta Shirya Auren Jama’a Ga Masu Shirin Sadaukar Da Rayukansu A Yaki

May 19, 2026

NUJ-FCT Ta Gargadi ‘Yan Jarida Kan Yada Labaran Karya Gabanin Zabuka

May 19, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Mummunar Hanyar Kauye Na Hana Yara Zuwa Makaranta A Akwa Ibom — Mazauna Yanki

June 5, 2026

Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

June 5, 2026

Dayo Amusa Ta Soki Matsin Lambar Da Ake Yi Wa Fitattun Jarumai Kan Matsalolin Kasa

June 5, 2026

Kungiya Ta Bukaci Hadin Kan ‘Yan Najeriya Wajen Yaki Da Matsalar Tsaro

June 5, 2026

TCN Ta Sanar da Katse Wutar Lantarki a Sassan Delta Saboda Ayyukan Gyaran Tashar Wuta

June 5, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.