Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    Najeriya Ta Kai Dala $18.4 Biliyan a Cinikayyar Cikin Afirka a 2024

    June 28, 2025

    Afreximbank Ta Ba Najeriya Tallafin $50 Biliyan Don Manyan Ayyuka

    June 28, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    Najeriya Ta Samu Jarin Waje Har Dala Biliyan 2.5 Daga Masarautar Saudiyya

    June 29, 2025

    Tiwa Savage Ta Bayyana Yadda Take Rashin Kulawar Don Jazzy Da Mavin

    May 20, 2026

    NERC Da ONSA Sun Hada Kai Don Dakile Lalata Kayan Wutar Lantarki

    May 20, 2026

    Iran Ta Shirya Auren Jama’a Ga Masu Shirin Sadaukar Da Rayukansu A Yaki

    May 19, 2026

    NUJ-FCT Ta Gargadi ‘Yan Jarida Kan Yada Labaran Karya Gabanin Zabuka

    May 19, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

    June 5, 2026

    Achievers University Ta Bankado Zargin Damfarar Kudin Makaranta Ta N457.5m

    May 25, 2026

    NYSC ta shawarci iyaye su taimaka wa ‘ya’yansu da karin kudin tafiya

    May 21, 2026

    NYSC ta tsawaita wa wasu masu bautar kasa hidima a Gombe

    May 21, 2026

    Najeriya da Italiya sun hada kai domin tara dala biliyan 5 don tallafa wa ilimi

    May 21, 2026
  • Health

    OYO TA KWANTAR WA MAZAUNA HANKALI KAN CUTAR EBOLA, TA SA MA’AIKATAN LAFIYA CIKIN SHIRI

    June 4, 2026

    Likitan Ondo Sun Ƙara Matsin Lamba Kan Gwamnati, Sun Yi Barazanar Tsunduma Yajin Aiki

    May 19, 2026

    Coroner’s Court ta dakatar da shari’ar mutuwar ɗan Chimamanda Adichie har sai umarnin Attorney-General

    May 5, 2026

    Sarki Charles III Ya Yarda Cewa Ciwon Kansar Da Ke Damunsa Na Iya Hana Shi Ganin Dogon Aikin Da Ya Kafa

    April 30, 2026

    Masana lafiya sun bukaci daukar matakin gaggawa kan cutar sickle cell a Najeriya da Afirka

    April 29, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Tinubu Torchbearers Zai Taimaka Wajen Wayar Da Kai Da Tallafawa Gwamnati — APC Women Leader

    June 4, 2026

    INEC Ta Shirya Tsaf Domin Zaben Sanatan Ondo Kudu Ranar 20 ga Yuni

    June 4, 2026

    LP Ta Kammala Zaben Fidda Gwani, Ta Tsayar da ‘Yan Takara na Majalisa a Anambra

    June 4, 2026

    Peter Obi Ya Kare Adeboye, Ya Gargadi Matasa Kan Rarrabuwar Kabilanci Da Addini

    June 4, 2026

    Tsohon Firaministan Senegal Ousmane Sonko Ya Zama Kakakin Majalisa

    May 26, 2026
  • Sports

    Shaibu Ya Yabawa Super Eagles Da Adeboye Kan Nasarorin Unity Cup Da Wasan Poland

    June 4, 2026

    Super Eagles Na Da Ƙarfin Doke Kowace Ƙasa Duk Da Rashin Tikitin Gasar Kofin Duniya

    June 4, 2026

    Kai Havertz Ya Yabawa Jamus Karfin ‘Yan Hari Gaban Gasar Kofin Duniya Ta 2026

    June 4, 2026

    Marinakis Ya Yi Rikici A Athens Yayin Gasar EuroLeague

    May 25, 2026

    Spurs Sun Farfado Thunder, Wembanyama Ya Jagoranci Nasara A Wasan NBA

    May 25, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Matatar man Ɗangote ta tarwatsa harkar shigo da tataccen mai Najeriya daga Belgium -Jakadan Belgium
News

Matatar man Ɗangote ta tarwatsa harkar shigo da tataccen mai Najeriya daga Belgium -Jakadan Belgium

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaAugust 10, 20254 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp

IMG 2536Jakadan ƙasar Belgian a Najeriya, Pieter Leenknegt, ya ce matatar man Dangote za ta shafi harkar shigo da tataccen mai Najeriya daga ƙasarsa da ma tsarin kasuwanci a tsakanin ƙasashen na wani lokaci.

Kafin fara aikin matatar man Ɗangote, Najeriya na kan gaba wajen shigo da man fetur daga kasar Belgium.

Sai dai matatar man Ɗangote wacce ta fara aiki a shekarar bara, ta yi iƙirarin cewa za ta iya samar da man da ake buƙata a Najeriya.

A cikin wata tattaunawa ta musamman da PREMIUM TIMES ta yi da mista Leenknegt, ya ce, ana ganin fara tace mai da Najariya ta yi zan rage yawan man da take shigo da shi daga Belgium sosai.

Ya bayyana hakan da “tasirin da kamfanin Ɗangote ke da shi” yana mai nuna babban giɓin da ƙasarsa za ta samu tsakaninta da Najeriya duk da kasancewarta ƙasa da ke sahun masu samar wa da ƙasar nan man fetur.

Ya ce, ana tunanin za a fara ganin wannan tasiri a kasuwancin kasashen biyu ne daga karshen shekarar 2025.

“A fili yake cewa (ayyukan matatar Ɗangote), na wani lokaci zai shafi kasuwancin da ke tsakanin ƙasashen nan biyu,” ya faɗa.

Duk da a shekarar 2024 an samu raguwar man da Najeriya ke saye daga kasar Belgium, jakadan ya alaƙanta hakan da rage amfani da makamashi da aka yi a ƙasar nan a maimakon cewa tasirin matatar Dangote ce.

“An samu raguwar fitar da kaya daga Belgium zuwa Najeriya, haka ma daga Najeriya zuwa Belgium,” ya bayyana.

“Amma ba tasiri matatar man Dangote ba ce. Batu ne na yanayin sayen makamashi a Najeriya wanda ya sa ‘yan ƙasar ba su da wadataccen Dala ko Yuro a hannunsu da za su bi sayi kaya daga waje.”

A yayin da yake nuna amincewarsa da rawar ƙasarsa na mamaye harkar shigo da mai Najeriya, jakadan ya ce, “mu ne kasar nahiyar Turai mafi shigo da kaya Najeriya, kuma mafi yawa danyen man fetur ne.”

Kusan kaso 40% na abin da Najeriya take saye daga waje yana wucewa ne ta Belgium, kuma yawanci tataccen man fetur ne.

Kuma Belgium babbar mai samar wa da Najeriya sinadarai ce da kayan kiwon lafiya da kayan amfani a masana’antu.

Game da matatar man Dangote:

Matatar man Dangote ita ce mafi girma a duniya wajen tace mai, kuma ta fara ne da ta ce man dizal da man jirgin sama a watan Janairun 2024 amma sai a Satumbar 2024 ta fara tace man fetur.

Fara aikin matatar ya jawo raguwa yawan man da ake shigo da shi Najeriya. Kuma ya jawo an rage kashe kuɗin waje.

A cewar hukumar kididdiga ta ƙasa (NBS), rahotanni sun nuna cewa Najeriya ta kashe Dala biliyan 1.2 wajen shigo da mai a rubu’in farko na shekarar 2025 ƙasa da Dala biliyan 2.6 da ta kashe a bara.

A watan Yuni, matatar ta sanar da fara sayar da man fetur da dizal ga ‘yan kasuwa da kamfanoni da kamfanonin sadarwa .da sauran masu sayen mai da yawan gaske.

A cikin watanni uku, matatar Dangote ta rage yawan farashin manta har sau biyu domin yin daidai da farashin mai a duniya. Da farko, a watan Yuni, daga N880 zuwa N840 na kowanne lita. Sai kuma a watan Yuli zuwa N8320 kowanne lita.

Kafin samar da kamfanin matatar Dangote, Najeriya ta dogara ne da shigo da mai daga kasar waje duk da ita ce kan gaba wajen samar da ɗanyen mai a Afirka.

Mista Leenknegt ya bayyana yawan dogaro da shigo da tataccen mai Najeriya da rashin kan gado.

“Ba lissafi a tafi da mai Turai daga Najeriya sannan a sake dakonsa daga Turai zuwa Najeriya. Ba lissafi sosai.”

“Daga lokacin da Najeriya ta iya samar da ingantaccen tataccen man fetur, wacce kuma kasar Belgium da za ta ƙalubalance ta?” Ya tambaya.

“Amma abin da za mu mai da hankali a kai shi ne kasuwancinmu da Najeriya zai karkata ne kan wasu abubuwa a nan gaba.”

Misata Leenknegt, ya ce Belgium tana tunanin karkata harkar shigo da kayan zuwa Najeriya daga harkar man fetur zuwa ga harkar noma.

Ya ce wannan sauyi wata hanya ce ta sauya kalar kasuwanci da Belgium ke shirin yi tsakaninta da Najeriya.

“Mun daɗe muna tunanin sake fasalin kasuwancinmu tun da daɗewa daga man fetur zuwa wani abu daban saboda bai kamata ƙasa ta ta’allaka tattalin arziƙinta da dogaro da mai ba,” ya faɗa.

A cikin wannan hira, jakadan ya tattauna wasu abubuwa da suka shafi samar da magunguna da noma da sauran harkokin kasuwanci.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleZan kawar da cin hanci a watan farko ko nayi murabus–Ameachi
Next Article Dalilin da ya sa gwamnan Abba na Kano ya kori wasu hadimansa 2

Related Posts

Tiwa Savage Ta Bayyana Yadda Take Rashin Kulawar Don Jazzy Da Mavin

May 20, 2026

NERC Da ONSA Sun Hada Kai Don Dakile Lalata Kayan Wutar Lantarki

May 20, 2026

Iran Ta Shirya Auren Jama’a Ga Masu Shirin Sadaukar Da Rayukansu A Yaki

May 19, 2026

NUJ-FCT Ta Gargadi ‘Yan Jarida Kan Yada Labaran Karya Gabanin Zabuka

May 19, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Mummunar Hanyar Kauye Na Hana Yara Zuwa Makaranta A Akwa Ibom — Mazauna Yanki

June 5, 2026

Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

June 5, 2026

Dayo Amusa Ta Soki Matsin Lambar Da Ake Yi Wa Fitattun Jarumai Kan Matsalolin Kasa

June 5, 2026

Kungiya Ta Bukaci Hadin Kan ‘Yan Najeriya Wajen Yaki Da Matsalar Tsaro

June 5, 2026

TCN Ta Sanar da Katse Wutar Lantarki a Sassan Delta Saboda Ayyukan Gyaran Tashar Wuta

June 5, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.