Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    Najeriya Ta Kai Dala $18.4 Biliyan a Cinikayyar Cikin Afirka a 2024

    June 28, 2025

    Afreximbank Ta Ba Najeriya Tallafin $50 Biliyan Don Manyan Ayyuka

    June 28, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    Najeriya Ta Samu Jarin Waje Har Dala Biliyan 2.5 Daga Masarautar Saudiyya

    June 29, 2025

    Tiwa Savage Ta Bayyana Yadda Take Rashin Kulawar Don Jazzy Da Mavin

    May 20, 2026

    NERC Da ONSA Sun Hada Kai Don Dakile Lalata Kayan Wutar Lantarki

    May 20, 2026

    Iran Ta Shirya Auren Jama’a Ga Masu Shirin Sadaukar Da Rayukansu A Yaki

    May 19, 2026

    NUJ-FCT Ta Gargadi ‘Yan Jarida Kan Yada Labaran Karya Gabanin Zabuka

    May 19, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

    June 5, 2026

    Achievers University Ta Bankado Zargin Damfarar Kudin Makaranta Ta N457.5m

    May 25, 2026

    NYSC ta shawarci iyaye su taimaka wa ‘ya’yansu da karin kudin tafiya

    May 21, 2026

    NYSC ta tsawaita wa wasu masu bautar kasa hidima a Gombe

    May 21, 2026

    Najeriya da Italiya sun hada kai domin tara dala biliyan 5 don tallafa wa ilimi

    May 21, 2026
  • Health

    OYO TA KWANTAR WA MAZAUNA HANKALI KAN CUTAR EBOLA, TA SA MA’AIKATAN LAFIYA CIKIN SHIRI

    June 4, 2026

    Likitan Ondo Sun Ƙara Matsin Lamba Kan Gwamnati, Sun Yi Barazanar Tsunduma Yajin Aiki

    May 19, 2026

    Coroner’s Court ta dakatar da shari’ar mutuwar ɗan Chimamanda Adichie har sai umarnin Attorney-General

    May 5, 2026

    Sarki Charles III Ya Yarda Cewa Ciwon Kansar Da Ke Damunsa Na Iya Hana Shi Ganin Dogon Aikin Da Ya Kafa

    April 30, 2026

    Masana lafiya sun bukaci daukar matakin gaggawa kan cutar sickle cell a Najeriya da Afirka

    April 29, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Tinubu Torchbearers Zai Taimaka Wajen Wayar Da Kai Da Tallafawa Gwamnati — APC Women Leader

    June 4, 2026

    INEC Ta Shirya Tsaf Domin Zaben Sanatan Ondo Kudu Ranar 20 ga Yuni

    June 4, 2026

    LP Ta Kammala Zaben Fidda Gwani, Ta Tsayar da ‘Yan Takara na Majalisa a Anambra

    June 4, 2026

    Peter Obi Ya Kare Adeboye, Ya Gargadi Matasa Kan Rarrabuwar Kabilanci Da Addini

    June 4, 2026

    Tsohon Firaministan Senegal Ousmane Sonko Ya Zama Kakakin Majalisa

    May 26, 2026
  • Sports

    Shaibu Ya Yabawa Super Eagles Da Adeboye Kan Nasarorin Unity Cup Da Wasan Poland

    June 4, 2026

    Super Eagles Na Da Ƙarfin Doke Kowace Ƙasa Duk Da Rashin Tikitin Gasar Kofin Duniya

    June 4, 2026

    Kai Havertz Ya Yabawa Jamus Karfin ‘Yan Hari Gaban Gasar Kofin Duniya Ta 2026

    June 4, 2026

    Marinakis Ya Yi Rikici A Athens Yayin Gasar EuroLeague

    May 25, 2026

    Spurs Sun Farfado Thunder, Wembanyama Ya Jagoranci Nasara A Wasan NBA

    May 25, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Dalilin da ya sa gwamnan Abba na Kano ya kori wasu hadimansa 2
News

Dalilin da ya sa gwamnan Abba na Kano ya kori wasu hadimansa 2

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaAugust 10, 20253 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp

IMG 2537Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kori wasu hadimansa biyi masu taimaka masa na musamman biyo bayan sakamakon kwamitin bincike da aka kafa domin bincikar kowannensu.

Wanann na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Kano, Umar Farouk Ibrahim, ya fitar a ranar Asabar.

Sakamakon wancan bincike, gwamnan ya amince da sallamar Abubakar Umar Sharada, babban mai taimaka masa kan harkokin siyasa bayan kwamitin bincike ya same shi da hannu wajen belin babban dilan ƙwaya Sulaiman Aminu Danwawu.

Kwamitin ya bankaɗo yadda Sharada ya bayar da shaida ta ƙashin kansa kan wannan gagarun dilan kwayan.

A cewar wasiƙar da sakataren gwamnatin Kano (SSG), ya fitar a ranar Juma’a, 8 ga Agustan 2025, an buƙaci Sharada ya miƙa dukkan kayan gwamnati da ke hannunsa ga sakataren dindin na ofishin mai bincike da tantancewa da harkokin siyasa (REPA) da ke ƙarƙashin ofishin sakataren gwamnatin, a ranar ko kafin Litinin, 11 ga watan Agustan 2025.

Sannan ana gargaɗinsa da kiran kansa da jami’an wannan gwamnati a ko’inna.

Haka kuma, gwamnan Kano ya sauke Tasiu Adamu Al’amin Roba, babban mai taimaka masa kan tafiyar da al’amuran gwamnat (Cabinet Office) bayan samunsa da laifin sauya buhunhunan hatsi na tallafi da ke ajiye a ɗakin ajiya a Sharaɗa tun a shekarar 2024.

Tun wannan lokaci ne Roba ke fuskantar shari’a a kotu bisa zargin laifin sata da haɗa kai wajen aikata babban laifi na karkatar da kayan gwamnati.

Shi ma Roba, an buƙaci ya miƙa duk wani abin amfani na gwamnati da ke hannunsa haɗi da shaidar fayyace kai (ID card) , a ranar ko kafin Litinin 11 ga watan Agustan 2025. Sannan ana gargaɗinsa da kauce wa kiran kansa da jami’in gwamnatin jihar Kano.

A wani makamancin al’amari, gwamnatin Kano ta wanke Hon. Musa Ado Tsamiya, babban mai taimaka wa gwamna kan magudanan ruwa daga zargin da ake yi masa wanda kwamitin binciken ya tabbatar cewa bai aikata kowanne irin laifi.

Gwamna Abba ya jaddada aniyar gwamnatinsa ta tabbatar da ɗa’a da gaskiya da cewa ba za ta lamunci kowanne irin nau’i na cin hanci da rashawa ba.

Ya kuma gargaɗi dukkan masu riƙe da muƙamai da yi riƙo da gaskiya a dukkan ayyukansu da suka shafi gwamnati da kuma na ƙashin kansu.

“Da wannan sanarwa, ana shawartar al’umma da su guje wa yin kowacce iriyar mu’amala da tsofaffin masu taimaka wa gwamnan da aka kora, musamman abin da ya shafi gwamnati. Kuma duk wanda ya yi hakan, to kar ya zargi kowa, sai kansa.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleMatatar man Ɗangote ta tarwatsa harkar shigo da tataccen mai Najeriya daga Belgium -Jakadan Belgium
Next Article wuce’Har yanzu Peter Obi ɗan Jam’iyyar Labour ne’

Related Posts

Tiwa Savage Ta Bayyana Yadda Take Rashin Kulawar Don Jazzy Da Mavin

May 20, 2026

NERC Da ONSA Sun Hada Kai Don Dakile Lalata Kayan Wutar Lantarki

May 20, 2026

Iran Ta Shirya Auren Jama’a Ga Masu Shirin Sadaukar Da Rayukansu A Yaki

May 19, 2026

NUJ-FCT Ta Gargadi ‘Yan Jarida Kan Yada Labaran Karya Gabanin Zabuka

May 19, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Mummunar Hanyar Kauye Na Hana Yara Zuwa Makaranta A Akwa Ibom — Mazauna Yanki

June 5, 2026

Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

June 5, 2026

Dayo Amusa Ta Soki Matsin Lambar Da Ake Yi Wa Fitattun Jarumai Kan Matsalolin Kasa

June 5, 2026

Kungiya Ta Bukaci Hadin Kan ‘Yan Najeriya Wajen Yaki Da Matsalar Tsaro

June 5, 2026

TCN Ta Sanar da Katse Wutar Lantarki a Sassan Delta Saboda Ayyukan Gyaran Tashar Wuta

June 5, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.