Rundunar ‘yan sandan Najeriya (NPF) ta yi watsi da zargin cewa an rasa bindigu 3,907 daga hannun jami’anta, tana mai bayyana hakan a matsayin wasa da hankali da kuma rashin gaskiya.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Alhamis, rundunar ta ce makaman da suka bata sun faru ne sakamakon hare-haren ‘yan ta’adda da masu aikata laifi kan jami’anta, tare da farmakin da ake kaiwa ma’ajiyarta.
Kakakin rundunar, ACP Muyiwa Adejobi, ya bayyana cewa suna kokarin kwato bindigun da aka sace, inda tuni suka bankado wasu daga cikin masu hannu a lamarin kuma sun mayar da makaman da aka samo.
Rundunar ta bayyana mamaki kan rahoton da ya ce an rasa bindigu 3,907 tun daga 2019, tana mai jaddada cewa ba haka lamarin yake ba, kuma ba a karkatar da makaman ba. Wannan martanin na zuwa ne bayan rahoton babban mai binciken kudi na gwamnatin tarayya da ya janyo rashin fahimta tsakanin rundunar da majalisar dattawa.
