Hukumar Yaki da Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa (EFCC) ta musanta rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa tana daukar sabbin ma’aikata a boye, tana mai bayyana cewa labarin karya ne.
A wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na hukuma na X a ranar Litinin, hukumar ta gargadi jama’a da su yi hattara da irin wadannan bayanan bogi.
Sanarwar ta kunshi hoto mai dauke da rubutun “FAKE NEWS” da kuma “THIS IS FALSE NEWS. BEWARE!”, domin bayyana cewa bayanin da ake yadawa ba gaskiya ba ne.
Jita-jitar da ake yadawa ta yi ikirarin cewa EFCC na daukar ma’aikata a boye tare da cewa wadanda aka dauka za su fara horo nan da wata mai zuwa, sannan ta bukaci mutane su rika aika sakonni ba tare da bayyana sunayensu ba.
Sai dai EFCC ta yi watsi da wannan ikirari, tana mai bayyana shi a matsayin labarin karya, tare da bukatar ‘yan Najeriya su yi watsi da shi gaba daya.
Hukumar ta bayyana cewa wannan gargadin ya zama dole ne saboda yadda masu damfara ke ci gaba da yada sanarwar daukar aiki ta bogi da sunan EFCC domin yaudarar masu neman aiki da kuma karbar kudi daga gare su.
EFCC ta sake jaddada cewa duk lokacin da za ta dauki sabbin ma’aikata, za ta sanar da jama’a ne ta hanyoyin sadarwarta na hukuma, ba a boye ba kuma ba ta hannun wasu mutane ko kamfanoni ba.
A karshe, hukumar ta bukaci jama’a su tabbatar da sahihancin duk wani bayani da ya shafi ayyukanta ta hanyar duba kafafen sadarwarta na hukuma kafin su dauki wani mataki.
