Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta ajiye hukunci kan ƙarar da African Democratic Congress (ADC) da wasu jam’iyyu huɗu suka shigar, suna ƙalubalantar hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ya umarci INEC ta cire su daga rajistar jam’iyyun siyasa.
Kwamitin alkalai uku ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Abba Bello Mohammed ya ce za a sanar da ɓangarorin ranar da za a yanke hukunci bayan lauyoyi sun kammala gabatar da hujjojinsu.
Jam’iyyun da abin ya shafa sun haɗa da ADC, Action Peoples Party (APP), Action Alliance (AA), Accord Party da Zenith Labour Party (ZLP).
Tun farko, Babbar Kotun Tarayya ta yanke hukuncin cewa jam’iyyun sun kasa cika sharuɗɗan kundin tsarin mulki na ci gaba da kasancewa a rajista, tare da hana INEC amincewa da ‘yan takararsu ko barinsu su shiga babban zaɓen shekarar 2027.
Sai dai jam’iyyun da kuma INEC sun ɗaukaka ƙara, suna neman Kotun Ɗaukaka Ƙara ta soke wannan hukunci.
A baya, Kotun Ɗaukaka Ƙara ta dakatar da aiwatar da hukuncin Babbar Kotun Tarayya har sai an yanke hukunci kan ƙarar, tare da sukar matakin da alkalin kotun farko ya ɗauka na ci gaba da sauraron shari’ar duk da umarnin dakatarwa da aka bayar.
Yanzu dai ana jiran ranar da Kotun Ɗaukaka Ƙara za ta bayyana hukuncinta kan makomar jam’iyyun kafin babban zaɓen shekarar 2027.
