Majalisar Wakilai ta Najeriya ta yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta tura cikakken shirin tsaro domin fatattakar ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane daga maboyarsu, tare da dawo da zaman lafiya a fadin ƙasar.
An yi wannan kiran ne bayan amincewa da wani kudiri na gaggawa da ɗan majalisa Ibe Osonwa ya gabatar a zauren majalisar a ranar Talata.
Kudirin ya nuna damuwa kan yawaitar hare-hare, sace ɗalibai da kuma tabarbarewar tsaro a makarantu da wuraren ibada a sassa daban-daban na Najeriya.
Dan majalisar ya ce gwamnati tana da alhakin kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada, yana mai cewa matsalar tsaro na ƙara tsananta a wasu yankuna.
Ya kuma bayyana cewa yawan sace ɗalibai ya tilasta wa yara da dama ficewa daga makaranta, lamarin da ke ƙara ta’azzara matsalar ilimi a ƙasar.
Majalisar ta kuma nuna damuwa kan yadda wuraren ibada suka koma wuraren kai hare-hare, inda masu ibada ke fuskantar barazana yayin gudanar da ayyukansu na addini.
Bayan tattaunawa, Majalisar Wakilai ta yi Allah-wadai da dukkan nau’o’in laifukan ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane a ƙasar.
Ta kuma umarci gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa mai ƙarfi domin tarwatsa maboyar ‘yan bindiga, tare da kare makarantu da wuraren ibada.
Majalisar ta kuma yi gargadi cewa idan gwamnati ta gaza shawo kan matsalar tsaro cikin wani ƙayyadadden lokaci, ya kamata a ɗauki matakin sauke shugabannin tsaro daga mukamansu.
Haka kuma, majalisar ta bai wa kwamitocinta umarnin sa ido kan aiwatar da wannan kudiri tare da gabatar da rahoto cikin makonni biyu.
