Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta bayyana cewa akalla mutane 13 ne suka rasa rayukansu sakamakon gobarar wuta, hadurran mota da kuma wasu hatsarori da suka shafi fadawa cikin tafkuna da rijiyoyi a fadin jihar cikin watan Mayun 2026.
Rahoton wata-wata na hukumar ya nuna cewa an samu gobara guda 58 a lokacin, tare da karɓar kiran gaggawa guda 80, ciki har da ayyukan ceto guda 15 da kuma kiran ƙarya guda bakwai.
Mai magana da yawun hukumar, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya ce jami’an kashe gobara sun gudanar da ayyukan ceto a dukkan ƙananan hukumomi 44 na jihar ta hanyar tashoshin kashe gobara guda 30.
A cewar rahoton, duk da asarar rayukan mutane 13, jami’an hukumar sun yi nasarar ceto mutane 34 daga hatsarori daban-daban a watan da ya gabata.
Hukumar ta kuma bayyana cewa gobarar da ta tashi a wurare daban-daban ta lalata dukiyoyin da darajarsu ta kai kusan Naira miliyan 144.01, yayin da saurin kai ɗauki ya taimaka wajen ceto dukiyoyin da suka kai darajar Naira miliyan 437.03.
Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Alhaji Sani Anas, ya buƙaci al’umma da su ƙara kula da matakan kariya daga gobara tare da yin taka-tsantsan wajen amfani da abubuwan da ka iya haddasa tashin wuta domin rage yawan afkuwar irin waɗannan bala’o’i a jihar.
