Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) a zaben 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya musanta zargin cewa yana taimaka wa kokarin sake zaben Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027.
Kwankwaso ya yi wannan bayani ne yayin wata hira da Global TV a daren Laraba, inda ya bayyana cewa zargin karya ne kuma yana rudani da tunzura jama’a.
Ya ce kalaman da mai magana da yawun Gwamnan Jihar Kano, Sanusi Bature, ya yi a Arise News cewa yana aiki a boye domin Tinubu, ba gaskiya ba ne.
A cewarsa, “Kawai wawaye ne za su yarda da irin wannan magana. Ba mu aiki da kowa. Muna aiki ne da NDC.”
Sai dai tsohon gwamnan Kano ya amince cewa yana da kyakkyawar dangantaka da Shugaba Tinubu, amma ya ce hakan ba yana nufin suna tafiya a siyasa daya ba.
“Bola Tinubu dan uwana ne kuma abokina na dade. Amma hakan ba ya nufin za mu hada manufofin siyasa,” in ji shi.
Kwankwaso ya kuma soki gwamnatin yanzu, yana mai cewa akwai yiwuwar shugaban kasa ba ya samun cikakken bayani kan halin da kasa ke ciki saboda wadanda ke kewaye da shi.
Ya ce, “A yawancin lokuta, shugaban kasa ba zai ga ainihin abin da ke faruwa ba. Abin takaici, yawancin wadanda ke kusa da shi su ne ke haddasa matsaloli.”
Ya kuma bayyana cewa akwai hadin gwiwar siyasa da ake ci gaba da yi a cikin kungiyar Nigeria Democratic Congress (NDC), inda ya ce sun amince da goyon bayan Peter Obi a matsayin dan takarar shugaban kasa daga kudu.
Kwankwaso ya ce kungiyar na da isasshen lokaci domin wayar da kan jama’a kafin zaben 2027, yana mai cewa za su ci gaba da kokarin hada kan ‘yan Najeriya domin cimma nasara a akwatin zabe.
