Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa kuma ɗan kasuwa a fannin makamashi, Gbenga Olawepo-Hashim, ya yi Allah-wadai da kisan fasto tare da sace masu ibada a wani hari da aka kai Cocin Christ Apostolic Church No. 2 da ke Eda Oniyo, karamar hukumar Ilejemeje a Jihar Ekiti.
Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga kusan bakwai ne suka kai farmaki wajen wani taron ibada na revival da misalin ƙarfe 7:30 na yamma, inda suka buɗe wuta da makamai masu ƙarfi, suka kashe faston da aka gayyata, sannan suka sace aƙalla mutane 13 daga cikin masu ibada.
Shaidu sun ce harin ya ɗauki kusan mintuna 40 yana gudana, lamarin da ya jefa al’umma cikin firgici tare da tilasta mutane tserewa don ceton rayukansu.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, Olawepo-Hashim ya bayyana lamarin a matsayin “abin firgita da tayar da hankali matuƙa,” yana mai nuna alhini kan mutuwar faston da kuma sace mutane marasa laifi.
“Tunani na da addu’o’i na suna tare da waɗanda aka sace, kuma ina tare da iyalansu a wannan lokaci mai raɗaɗi,” in ji shi.
Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin fasto, cocin, da kuma al’ummar Eda Oniyo da makwabtansu.
Damuwar Jinkirin Aikin Tsaro
Olawepo-Hashim ya nuna damuwa kan rahotannin da ke cewa an samu jinkiri wajen mayar da martanin jami’an tsaro duk da kiraye-kirayen gaggawa da aka yi yayin harin, yana mai cewa da an kai ɗauki da wuri da an rage girman asarar da aka samu.
Duk da ya amince da cewa ana ci gaba da aikin bincike da ceto a dazukan da ke kusa, ya jaddada bukatar a inganta tsarin tsaro mai dogaro da bayanan sirri da kuma matakan rigakafi.
“Al’ummominmu ba za su ci gaba da rayuwa ƙarƙashin rahamar ‘yan ta’adda ba. Wuraren ibada dole ne su kasance wuraren zaman lafiya, ba filin tashin hankali ba,” in ji shi.
Kira ga Inganta Tsaro
Ya bukaci hukumomin tsaro da su ƙara ƙaimi wajen ceto waɗanda aka sace tare da kamo masu laifi domin gurfanar da su gaban shari’a.
Haka kuma ya shawarci gwamnatoci a dukkan matakai da su ƙarfafa tsarin tsaron yankuna, su inganta tsarin gaggawar ɗaukar mataki, da kuma dawo da kwarin gwiwar jama’a kan kare rayuka da dukiyoyi.
Ƙarin Damuwa Kan Tsaro
Harin ya ƙara tayar da hankalin jama’a kan matsalar rashin tsaro a yankunan karkara, musamman a wasu sassan Kudu maso Yamma da Arewa, inda ake ci gaba da samun hare-hare da sace-sacen mutane.
A watannin baya-bayan nan, an samu irin wannan hare-hare a wasu al’ummomi da wuraren ibada, lamarin da ya sa ake ƙara kiran gwamnati da hukumomin tsaro da su inganta sa ido da tattara bayanan sirri da kuma saurin mayar da martani.
Rahotanni sun ce mazauna Eda Oniyo na cikin fargaba yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da bincike a dazukan da ke kewaye domin gano waɗanda aka sace
