Dan Majalisar Wakilai mai wakiltar Jema’a/Sanga a Jihar Kaduna, Daniel Amos, ya yabawa jajircewa da kwazon ma’aikatan Najeriya duk da matsin tattalin arziki da ake fuskanta a ƙasar.
A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a domin bikin Ranar Ma’aikata, Amos ya nuna godiya ga ma’aikata a sassa daban-daban bisa jajircewarsu, ladabinsu da kuma sadaukarwar da suke yi wajen ci gaban ƙasa duk da ƙalubalen rayuwa.
Ya ce ma’aikatan Najeriya sun ci gaba da nuna ƙwazo da juriya duk da hauhawar farashi, rashin tabbas a wuraren aiki da sauye-sauyen tattalin arziki da ake samu.
Amos ya ce:
“Daga gonaki da ke samar da abinci, zuwa makarantu da ke gina makomar ƙasa, da asibitoci da ke ceton rayuka, da kasuwanni da ke tafiyar da tattalin arziki — ma’aikata su ne ginshiƙin ci gaban ƙasarmu.”
Ya ƙara da cewa gina ƙasa ba ya dogara da manufofi kaɗai, sai dai da ƙoƙari da sadaukarwar da jama’a ke yi a kullum, ko da ba a yawan jin labarinsu.
Dan majalisar ya jaddada cewa gudunmawar ma’aikata a muhimman fannoni na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da daidaiton zamantakewa da tattalin arziki a ƙasar.
A cewarsa, wajibi ne gwamnatoci a dukkan matakai da sauran masu ruwa da tsaki su ba da fifiko ga walwalar ma’aikata ta hanyar samar da manufofin da za su inganta albashi, kare haƙƙi da ƙara ingancin aiki.
Ya ce: “Yana da matuƙar muhimmanci a samar da yanayi mai kyau da zai tallafa wa ma’aikata, kare walwalarsu da ƙara musu ƙwazo.”
Amos ya kuma bayyana jajircewar ma’aikatan Najeriya a matsayin abin ƙarfafa gwiwa, yana mai cewa gudunmawarsu na taka muhimmiyar rawa wajen ci gaban ƙasa, musamman a Jihar Kaduna da mazabarsa ta Jema’a/Sanga.
Ya shawarci ma’aikata da su ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukansu domin ci gaban ƙasa.
