Uwargidan Gwamnan Jihar Anambra, Dr. Nonye Soludo, ta taya ma’aikatan Najeriya murnar Ranar Ma’aikata ta 2026, inda ta bayyana aiki a matsayin ginshiƙin kowace al’umma mai ci gaba, tare da cewa ma’aikata su ne ginshikin bunƙasar tattalin arziƙi da ci gaban ƙasa.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a, ta ce bikin Ranar Ma’aikata na bana yana kawo “sabon kuzari” da sabuwar himma daga gwamnati, masu ɗaukar aiki da kuma al’umma baki ɗaya domin tabbatar da cewa ana kare ma’aikata, ana girmama su, kuma ana ba su ladan da ya dace.
Dr. Soludo, wacce ita ce wacce ta kafa ƙungiyar sa-kai mai suna Healthy Living with Nonye Soludo, ta bayyana ma’aikata a matsayin “gwarzayen gaske” tare da kira ga hukumomi da su ƙara mayar da hankali kan jin daɗinsu da yanayin aikin su.
Ta jaddada muhimmancin ɗan Adam a ci gaban ƙasa inda ta ce:
“Ga duk wata hannu da ta taɓa riƙe kayan aiki, ɗaukar kaya, rubutu cikin dare, share ƙasa, kula da marasa lafiya, koyar da yara, ko kuma gina wani abu da ya fi kansa girma—wannan rana taku ce.”
Ta kuma sake tabbatar da goyon bayanta ga ma’aikatan Najeriya, tana mai cewa su ne ginshiƙin ci gaban ƙasa kuma ya kamata a riƙa girmama su ba kawai a Ranar Ma’aikata ba, har ma kowace rana.
Ta ce, “Aiki shi ne ginshiƙin kowace al’umma mai ci gaba. Bayan kowace hanya, kowace makaranta, kowace gona, da kowace hukuma, akwai himmar ma’aikacin Najeriya.
“Ba ku ɓoye ba. Ku ne ginshiƙin ci gabanmu, kuma sadaukarwar ku ta cancanci yabo da karramawa ba yau kaɗai ba, har kullum. Ku ne jaruman gaskiya na duniya.
“Yayin da muke shiga sabon wata, watan Mayu ya zo da sabon kuzari—sabuwar niyya daga gwamnati, masu aiki da jama’a gaba ɗaya domin tabbatar da kariya, girmamawa da lada ga ma’aikata.
“Ga ma’aikatan Jihar Anambra da Najeriya baki ɗaya, muna ganin ku, muna taya ku murna kuma muna girmama ku. Barka da Ranar Ma’aikata da Barka da Sabon Wata.”
