Sanata mai wakiltar Babban Birnin Tarayya (FCT), Ireti Kingibe, ta karyata zargin da ake mata cewa ta karɓi kuɗi domin taimakawa wajen wata bogon kwangilar Gwamnatin Tarayya, inda ta bayyana cewa waɗannan zarge-zargen ƙarya ne kuma basu da tushe ko makama.
A cikin wata sanarwa da ta sanya hannu da kanta, kuma ta fitar ga manema labarai a Abuja ranar Laraba, Sanatar ta ce ba ta taɓa neman ko karɓar kuɗi kan kowace kwangila ba, haka kuma ba ta taɓa ba wani izini ya yi aiki a madadinta a wannan fanni ba.
Ta ce rahoton da wata jarida ta fitar wanda ke cewa an gurfanar da ita a gaban hukumar yaki da rashawa ta ICPC kan zargin karɓar Naira miliyan 100 a matsayin cin hanci dangane da bogon kwangila, ƙarya ce tsagwaronta kuma tana da shakku kan dalilin fitowar wannan rahoto.
Sanatar ta ce ba ta taɓa samun gayyata, tambaya, ko bincike daga ICPC kan wannan batu ko wani makamancinsa ba.
Ta kuma bayyana cewa a matsayinta na Sanata, ba ta da ikon raba ko bayar da kwangila, domin dukkan ayyukan gwamnati ana gudanar da su ne ta ma’aikatun gwamnati kamar Ministoci da sauran hukumomi.
A cewarta, duk wanda ya danganta ta da bayar da kwangila ko karɓar cin hanci, ko dai bai fahimci yadda tsarin gwamnati ke aiki ba ne, ko kuma yana ƙoƙarin bata mata suna ne da gangan.
Ta kuma nuna damuwa kan lokacin da aka fitar da rahoton, inda ta ce ya fito ne jim kaɗan bayan wata hira da ta yi a gidan talabijin na ARISE TV, inda ta yi magana kan halin ƙasar da kuma bayyana matsalolin gwamnati.
Sanatar ta ce wannan na nuna akwai yunkurin dakile masu fadin gaskiya da kuma kai hare-haren bata suna ga ‘yan siyasa masu sukar gwamnati.
Ta kara da cewa ba za ta yi shiru ba, kuma za ta ci gaba da tsayawa kan gaskiya, gaskiya da riƙon amana a shugabanci.
A karshe, ta ce duk irin wadannan hare-hare ba za su hana ta ci gaba da bayyana ra’ayinta ba, domin al’ummar Najeriya na bukatar shugabanni masu gaskiya da jajircewa wajen fadin gaskiya.
