Shugaban ƙasar Kenya William Ruto ya kare kalamansa da suka jawo cece-kuce kan matakin kwarewar Ingilishi da ilimi a ƙasashen Afirka, yana mai cewa an fassara su ba daidai ba ne.
Da yake magana a taron Mining Investment Conference and Expo da aka gudanar a Nairobi, Ruto ya ce kalaman nasa an yi su ne a wata tattaunawa ta sirri wadda daga baya aka fitar da ita ga jama’a ba tare da cikakken bayani ba.
Ya ce: “Ka gaishe min da Minista, ka kai gaisuwa ga Shugaba Tinubu abokina, da kuma al’ummar Najeriya, waɗanda su ne surukaina, ka yi hakan da Ingilishi mai kyau.”
Ruto ya bayyana cewa manufarsa ita ce yin bayani kan yadda ake amfani da Ingilishi a Afirka gaba ɗaya, ba don cin mutuncin wata ƙasa ba.
“Na yi magana ne kan yadda mu a Afirka muke amfani da Ingilishi mai kyau. A wasu ƙasashe kamar Najeriya, idan ba ka iya Ingilishi sosai ba, irin namu na Kenya, za ka iya bukatar mai fassara,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa an fitar da maganar daga mahallinta na asali, wanda ya jawo cece-kuce a kafafen sada zumunta.
“An fassara abin ba daidai ba. Amma yana da kyau mu tattauna irin wannan batu,” in ji shi.
Wannan bayanin na zuwa ne bayan wani bidiyo da ya bazu a intanet da ake danganta shi da Ruto, inda ya yi magana kan tsarin ilimi na Kenya tare da kwatanta shi da na Najeriya.
Rahotanni sun nuna cewa kalaman sun jawo martani daga bangarori daban-daban, musamman a kafafen sada zumunta, inda ake tattauna dangantakar kalaman shugabannin Afirka.
Har yanzu ba a samu wata sanarwa ta hukuma daga gwamnatin Kenya ko Najeriya kan lamarin ba.
