Nasarawa State Governor, Abdullahi Sule, ya caccaki wasu ‘yan siyasa da ke bayyana biyan albashi da gina hanyoyi a matsayin manyan nasarorin mulki, yana mai cewa hakan ba shi ne ainihin jagoranci ba.
Gwamnan ya yi wannan jawabi ne a wajen taron lacca karo na 59 a Nasarawa State University, Keffi, inda ya ce shugabanci ya kamata ya wuce ayyukan da aka saba yi na gwamnati.
Ya ce:
“Ayyukan da ba su da tasiri kai tsaye ga al’umma ba su kamata a dauke su a matsayin nasara ba. Idan kana cewa kana biyan albashi ko gina hanyoyi a matsayin nasara, hakan ba shugabanci bane na gaskiya.”
A cewarsa, abubuwan da gwamnati ta saba yi kamar biyan ma’aikata da samar da ababen more rayuwa bai kamata a dauke su a matsayin abin alfahari ba, domin hakan aikin da aka zabe su yi ne tun farko.
Ya kara da cewa shugabanni su rika tunanin hanyoyin kirkire-kirkire da za su kawo sauyi kai tsaye ga rayuwar al’umma maimakon ayyukan da aka saba.
Sule ya bayar da misali da matsalar gobara a kasuwanni, inda ya ce gwamnati a baya tana bayar da tallafi duk lokacin da gobara ta tashi, amma hakan bai warware matsalar ba.
A cewarsa, gwamnati daga baya ta yanke shawarar gina kasuwar zamani domin dakile yawan gobarar da ke faruwa, wanda ya kawo karshen matsalar.
Ya kuma bayyana cewa gwamnatin sa ta yi amfani da karin kudin shiga na cikin gida wajen gina gada a Auta kusa da Keffi domin rage matsalar ambaliya.
A wajen taron, shugaban Nigerian Institute of Public Relations, Dr Ike Neliaku, ya yaba da kokarin gwamnan wajen ci gaban ababen more rayuwa a jihar.
Haka kuma, mataimakin shugaban NIPR, Prof Emmanuel Dandaura, ya gargadi cewa rashin daidaito tsakanin magana da aiki na iya rage amincewar jama’a ga gwamnati.
