Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Adamawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da aikata fashi da makami a karamar hukumar Yola-North.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Suleiman Nguroje, ya fitar a ranar Talata, ya ce jami’an ofishin ‘yan sanda na Doubeli sun gudanar da kamen a lokuta daban-daban kan laifuka biyu da ke da alaka da fashi.
Sanarwar ta bayyana cewa a ranar 3 ga watan Yuni, 2026, an kama Idris Auwal mai shekaru 22 mazaunin Doubeli Culvert, wanda ake zargi da haɗa baki da wasu mutum uku da suka tsere wajen satar wani shago a Nassarawo Borehole.
An ce sun kwashe jaka mai dauke da kudi, takardu masu muhimmanci da kayan shago da ba a bayyana darajarsu ba.
Binciken farko ya nuna cewa wanda aka kama ya amsa cewa suna aiki tare da wasu abokan aikinsa da ake ci gaba da neman su.
A wani lamari makamancin haka a ranar 5 ga watan Yuni, an kama wani da ake zargi da kasancewa mamba a ƙungiyar “Shilla” da ke addabar jama’a a yankin.
An ce ya tare wani Abubakar Abdullahi a hanyar Doubeli Bypass dauke da adda, inda ya sace masa wayar Itel da kuma Naira 19,000, sannan ya ji masa rauni a kai.
Sai dai jami’an ‘yan sanda sun isa wurin cikin gaggawa, suka kama wanda ake zargi tare da kai wanda aka jikkata asibiti domin kula da lafiyarsa.
Rundunar ta ce an kwato adda, wuka da kuma wayar da aka sace, yayin da ake ci gaba da bincike domin kama sauran wadanda ke da hannu a laifukan.
Kwamishinan ‘yan sanda ya jaddada aniyar rundunar wajen yaki da fashin “Shilla” da sauran laifuffuka, tare da kira ga jama’a da su rika bayar da bayanai masu amfani domin taimakawa tsaro
