Gwamnatin Jihar Oyo ta fara rushe wani ginin da ake zargin mafakar masu garkuwa da mutane ne da ke cikin ƙauyen Lakoun, a kan hanyar Ayegun–Olojuoro a birnin Ibadan.
An gano ginin ne a matsayin cibiyar da ake amfani da ita wajen tsare Mrs. Olaide Adegoke John-Paul, ‘yar uwar tsohon Ministan Wutar Lantarki, Cif Adebayo Adelabu, tare da ‘ya’yanta tagwaye masu shekaru 12 kafin a ceto su a karshen mako.
Rahotanni sun nuna cewa rushe ginin na daga cikin matakan gwamnatin jihar na fatattakar masu aikata laifuka da kuma lalata dukkan wuraren da ake amfani da su wajen aikata garkuwa da mutane a jihar.
Hukumomi sun ce wannan mataki na nuni da ƙudirin gwamnati na tabbatar da tsaro da kuma hana sake amfani da irin wadannan wurare wajen aikata laifuka a nan gaba.
Gwamnatin ta kuma jaddada cewa za ta ci gaba da aiki tare da hukumomin tsaro domin gano tare da hukunta duk masu hannu a aikata garkuwa da mutane a jihar.
