Gwamnatin tarayya da World Bank sun amince da soke dala miliyan 717.7 na kudaden tallafin da ba a kashe ba a karkashin shirin farfado da bangaren wutar lantarki a Najeriya.
Rahotanni sun bayyana cewa an soke ragowar kudaden ne daga cikin shirin Power Sector Recovery Programme (PSRP) mai darajar dala biliyan 1.52, bayan wasu muhimman gyare-gyare da aka tsara sun kasa cika.
An fara shirin ne a shekarar 2020 domin inganta harkar wutar lantarki, rage matsin kudi a gwamnati da kuma kara gaskiya a tsarin samar da wuta.
Bankin Duniya ya ce duk da wasu nasarori da aka samu, karin kudaden tallafin da aka amince da su a shekarar 2023 sun fuskanci matsaloli wajen aiwatar da sharuddan da suka dace domin sakin kudaden.
Rahoton ya nuna cewa daga cikin kudaden karin tallafin, kaso tara cikin dari kacal aka samu damar kashewa.
Bankin ya alakanta matsalolin da kalubalen da bangaren wutar lantarki ke ci gaba da fuskanta, ciki har da matsalolin rarraba wuta, karancin karfin layin sadarwa, da kuma rashin daidaiton kudaden shiga da kashewa.
Haka kuma sauyin tsarin canjin kudin kasashen waje da aka yi a shekarar 2023 ya janyo faduwar darajar naira, lamarin da ya kara tsadar iskar gas da ake amfani da ita wajen samar da wuta.
A cewar Bankin Duniya, gibin kudaden tallafin lantarki ya karu daga naira biliyan 140 a shekarar 2022 zuwa kusan naira tiriliyan 1.9 a shekarun 2024 da 2025.
An kuma bayyana cewa jinkirin aiwatar da wasu tsare-tsare da matsalolin tantance ayyuka sun rage damar sakin karin kudaden.
Saboda haka ne aka yanke shawarar kawo karshen shirin tun kafin wa’adin da aka tsara, inda aka mayar da ranar rufe shirin zuwa 31 ga Mayun 2026.
Tun da farko, Akanta Janar na Tarayya, Dr. Shamseldeen Ogunjimi, ya gargadi Bankin Duniya kan jinkirin amincewa da bayar da rancen da Najeriya ke nema, yana mai cewa hakan na iya sa kasar ta rage karbar irin wadannan rance a gaba
