Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya yi tsokaci cikin raha yana cewa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta kusan “mutuwa” sakamakon yawaitar ficewar ‘yan majalisa zuwa wasu jam’iyyu.
Akpabio ya bayyana hakan ne a zaman majalisa ranar Talata, bayan an sanar da sauya sheƙar wasu ‘yan majalisa daga ADC zuwa wasu jam’iyyu ciki har da Nigerian Democratic Congress (NDC) da Labour Party.
Ya ce yawan sauya sheƙa na ‘yan siyasa ya fara zama abin dariya a majalisa.
“Da alama ADC ta mutu. Ya kamata duk masu ficewa su haɗa takardunsu a kawo gaba ɗaya, kada mu riƙa maimaita sanarwa,” in ji shi cikin raha.
Akpabio ya ƙara da cewa: “Sau nawa mutum zai sauya jam’iyya a wata guda? Sau ɗaya ne, amma wasu har sau uku suke yi.”
Ya kuma ba da shawarar cewa ya kamata a dinga haɗa jerin masu sauya sheƙa a lokaci guda domin rage yawan sanarwa a zauren majalisa.
A zaman, Akpabio ya kuma karanta wasikar ficewar Sanata Enyinnaya Abaribe, wanda ya sauya jam’iyya daga APGA zuwa ADC sannan yanzu zuwa Labour Party.
A halin da ake ciki, ana ci gaba da sauya sheƙar ‘yan siyasa a majalisar dokokin ƙasa, inda aka ce fiye da ‘yan majalisa 17 na Majalisar Wakilai sun fice daga ADC zuwa NDC.
Sanata Victor Umeh da wasu sun bayyana cewa rikice-rikicen cikin gida da shari’o’in da ke ci gaba a ADC ne ya sa suka fice daga jam’iyyar.
