An shigar da Darma zauren Majalisar Dattawa da misalin ƙarfe 12:32 na rana, inda ya bayyana gaban ‘yan majalisa domin tantancewa kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ‘yan majalisa sun fara yi masa tambayoyi kan ƙwarewarsa, manufofinsa, da kuma shirinsa na tafiyar da ma’aikatar Gidaje da Cigaban Birane.
Wannan tantancewa na zuwa ne bayan Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya aike da takardar neman amincewar majalisar a ranar Laraba domin tabbatar da Darma a matsayin minista.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya karanta takardar a zaman majalisar, sannan ya tura batun zuwa kwamitin majalisa gaba ɗaya domin ci gaba da nazari, tare da umartar su da su kawo rahoto “da wuri-wuri.”
Muttaqha Darma, injiniya ne mai horo, wanda ya kammala digiri a fannin Injiniyan Injiniya (Mechanical Engineering) daga Jami’ar Bayero Kano. Ana sa ran zai kawo ƙwarewar fasaha wajen tafiyar da ma’aikatar da ke da muhimmanci wajen magance ƙarancin gidaje da matsalolin ci gaban birane a Najeriya.
Sai dai nadin nasa ya zo ne tare da tarihin siyasa mai cike da cece-kuce. A zaben 2023, Darma ya kasance mataimakin ɗan takarar gwamna a jam’iyyar NNPP, amma daga baya aka kore shi bayan ya nuna goyon baya ga ɗan takarar APC, Dikko Radda, a wani taro da jam’iyyar ta bayyana a matsayin wanda ba shi da izini.
Duk da haka, wasu na ganin nadinsa yana nuna ƙoƙarin gwamnati na amfani da ƙwararru a ma’aikatun da ke da alaƙa da ci gaban ababen more rayuwa, musamman a fannin gidaje inda ake fama da ƙarancin gidaje a manyan birane.
Ana sa ran Majalisar Dattawa za ta kammala tantancewar nan ba da jimawa ba, sannan ta yanke hukunci kan amincewa ko kin amincewa da nadin.
