Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo, ya bayyana alhini mai zurfi kan rasuwar Brigadier Janar Oseni Braimah, yana mai bayyana hakan a matsayin babban rashi ga jihar da ma ƙasa baki ɗaya.
A cikin saƙon ta’aziyya da aka fitar a ranar Asabar ta bakin Mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Patrick Ebojele, gwamnan ya yaba da irin gudunmawar da marigayin ya bayar, yana mai kiran sa ɗan asalin Edo mai kishin ƙasa wanda ya rasu yana cikin hidimar ƙasa.
Okpebholo ya ce marigayin ya kasance abin koyi wajen jarumtaka, ladabi da kuma cikakken sadaukarwa ga aiki, yana mai ƙara da cewa ya sadaukar da rayuwarsa domin tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da tsaron ƙasar nan har zuwa ƙarshe.
Ya kuma bayyana marigayin a matsayin alamar sadaukarwa da kishin ƙasa, yana mai cewa rayuwarsa da aikinsa sun nuna muhimman darajoji da ƙasa ke dogaro da su.
Ya ce:
“Wannan rashi ba na rundunar sojin Najeriya kaɗai ba ne, har ma da jihar Edo da ƙasa baki ɗaya. Duk da muna cikin jimami, muna alfahari da rayuwar da ya yi da kuma hidimar da ya bayar.”
Gwamnan ya miƙa ta’aziyya ga iyalan marigayin, rundunar sojin Najeriya da dukkan waɗanda wannan rashi ya shafa, yana mai roƙon su da su samu ƙarfafawa daga kyakkyawan tarihin rayuwa da marigayin ya bari a baya.
