Hukumar hana safarar mutane ta ƙasa (NAPTIP) ta ceto wata mata mai shekaru 36 daga zargin cin zarafin aure a yankin Asokoro Extension da ke Abuja.
-
A cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na X a ranar Alhamis, ta bayyana cewa rundunar ta Rapid Response Squad ce ta kai dauki bayan samun sahihan bayanai kan lamarin.
Hukumar ta ce wanda ake zargi, mai suna Mista Godwin, mai shekaru 48 kuma mijin matar, ana zarginsa da dukan matar. An kuma bayyana cewa sun shafe shekaru 22 suna aure.
Sanarwar ta kara da cewa, ma’auratan dukkansu ‘yan asalin Kenshishe ne a jihar Benue.
NAPTIP ta ce jami’anta sun samu nasarar ceto matar daga wannan hali na cin zarafi, inda aka kai ta wuri mai aminci domin samun kulawa da taimako da ya dace.
Hukumar ta kuma tabbatar da cewa ta fara gudanar da bincike kan lamarin, tare da daukar matakan doka da suka dace domin tabbatar da adalci.
NAPTIP ta jaddada kudurinta na kare masu rauni a cikin al’umma, tana mai cewa za ta ci gaba da tabbatar da mutunci, tsaro da hakkokin kowa da kowa a fadin ƙasar.
Hukumar ta kuma yi kira ga jama’a da su rika kai rahoton duk wani nau’i na cin zarafi ko tashin hankali a cikin gida domin daukar matakin gaggawa.
