Gwamnatin tarayya ta ce Shugaba Bola Tinubu ya nuna adalci wajen rabon ayyuka da nade-nade a dukkan yankunan ƙasar.
Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris ne, ya bayyana haka a ranar Lahadi, inda ya ce rade-radin cewa Shugaba Tinubu na fifita wasu yankuna “ƙarya ce da wacce babu gaskiya a ciki.”
A cewarsa, gwamnatin Tinubu ta tabbatar da daidaito a rabon manyan ayyuka kamar hanyoyi, gadoji, layin dogo da cibiyoyin kiwon lafiya, tare da samar da fiye da guraben aiki 250,000.
Idris ya ce Arewa maso Yamma ce ta fi cin gajiyar ayyukan da aka amince da su, inda ta samu sama da kashi 40% na jimillar kuɗaɗen ayyuka, wato Naira tiriliyan 5.97.
Yankin Kudu maso Kudu ya samu Naira tiriliyan 2.41, Arewa ta Tsakiya Naira tiriliyan 1.13, Kudu maso Gabas Naira biliyan 407, Arewa maso Gabas Naira biliyan 400, yayin da Kudu maso Yamma (banda Lagos) ta samu Naira biliyan 604.
Ya kuma bayyana cewa adalci ya bayyana a nade-naden shugaba Tinubu, tare da kafa sabbin hukumomin raya yankuna guda biyar da ma’aikatar kiwon dabbobi.
Ministan ya jaddada cewa Tinubu na gina manyan ayyukan kasa domin kowa ya ci gajiyar su, yana mai cewa: “Babu wani yanki da za a bari a baya.”