Mahukuntan Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta gwamnatin tarayya da ke jihar Bauchi sun rufe makarantar bayan wata zanga-zanga da ɗaliban makarantar suka gudanar a yau Talata.
Hukumar makarantar ta ce wasu ɓata-gari sun shiga cikin ɗaliban da ke zanga-zangar tare amfani da damar wajen neman tayar da zaune tsaye, kuma saboda hakan ne ta rufe makarantar nan take.
Kungiyar ɗaliban makarantar ta ce sun yi zanga-zangar ne game da yadda ake shiga makarantar tare da sace musu kayayyakinsu, tare da raunata wasunsu.
A daren ranar Litinin ne wasu da ake zargi ɓarayi ne suka kutsa cikin makatarantar tare da yi wa ɗaliban fashi da makami, har ta kai ga an raunata biyu daga cikinsu.