Gwamnatin tarayya ta gargadi Kano da sauran jihohin arewa akan ambaliya
Malam Bokani ya roƙi mazauna yankuna, hukumomin kananan hukumomi da sauran hukumomi masu ruwa da tsaki su dauki matakan kariya tun kafin faruwar ambaliyar, tare da samar da rahotanni cikin lokaci don a samu damar daukar matakan gaggawa idan ambaliya ta faru.
Wannan gargadi ya biyo bayan wani irin irin gargadin da aka fitar a watan da ya gabata ga jihohi 11, lamarin da ke nuna cewa akwai buƙatar ci gaba da kula da shirin kare kai a yankin Arewa.