Tsohon Ministan Sadarwa na Najeriya, Farfesa Isa Ali Pantami, ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta karrama dalibar jihar Yobe, Nafisa Abdullah Aminu, wadda ta lashe Gasar Turanci ta Duniya, da kyautar dala 100,000, gida, da kuma lambar girmamawa ta OON (Officer of the Order of the Niger).
Pantami ya bayyana hakan ne a cikin wani sako da ya wallafa a safiyar Talata, inda ya yaba da hazaka da bajintar Nafisa, ’yar shekara 15, wadda ta wakilci Najeriya a gasar da ta gudana a kasar Malaysia, inda ta zo ta daya a duniya.
Ya ce wannan nasara babbar alfahari ce ga Najeriya, kuma ya dace gwamnati ta yaba da hakan ta hanyar kyauta mai daraja da kuma karramawa.
Tsohon ministan ya kuma bukaci a gayyato Nafisa da malamanta na harshen Turanci zuwa Fadar Shugaban kasa domin a karrama su bisa gudunmawar da suka bayar.
A cewarsa, malaman sun cancanci irin kyautar da aka bai wa masu horas da ’yan wasan kwando na Najeriya D’Tigress wadanda aka ba su gida, dala 50,000 kowannensu, da kuma lambar girmamawa.
Wannan kira na Pantami na zuwa ne kwana guda bayan Gwamnatin Tarayya ta karrama ‘yan wasan kwallon kwando mata ta D’Tigress da kyaututtuka masu tsoka, bayan nasarar da suka samu a gasar Kofin Afirka na shekarar 2025.
Kasa da mako guda da gwamnatin ta karrama tawagar Super Falcons, bayan sun lashe gasar kwallon kafa ta Afirka