A ranar Laraba ne Atiku ya sanar da sauya sheƙa daga jam’iyyar PDP, inda ya yi zargin cewa ta sauka daga turba na asali da aka kafata a kai.
Ministan sufurin jiragen sama da bunƙasa harkokin samaniya na Najeriya, Festus Keyamo ya soki tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, kan sauya sheƙa da ya yi daga jam’iyyar PDP a daidai lokacin da ake makokin rasuwar marigayi shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
A wani sako da Keyamo ya wallafa a shafin X, ya yi Alla-wadai da matakin da Atiku ya ɗauka inda ya ce yana son karkatar da hankalin ƴan ƙasa daga zaman makoki da ake yi.
“Duk da cewa yana da hakkin da kundin mulki ya ba ka na sauya jam’iyyar siyasa a kowane lokaci da kake so, amma sanar da sauya sheƙa daga PDP a wannan mako da ake makokin rasuwar tsohon shugaban ƙasa Buhari, yunkuri ne kawai na karkatar da hankalin mutane daga abin da ke faruwa zuwa kansa.
“Hakan ya nuna ƙarara cewa buƙatar da kake so ta zama shugaban ƙasa ba ta da tausayi ko kuma jimami,” kamar yadda Keyamo ya rubuta.
Sai dai mai magana da yawun Atiku Abubakar, Paul Ibe, ya kwatanta kalaman Keyamo da cewa maganganu ne na son rai.
“Ina Keyamo yake lokacin da Atiku yake jagorantar sojoji a fagen daga? Ina yake? Ɓabatu kawai yake yi, kuma lokacin yin maganganu na son rai ya zo karshe,” in ji Paul Ibe yayin tattaunawa da gidan talabijin na Channnels.
