Shugaban Hukumar Ilimin Firamare ta Jihar Nasarawa (NSUBEB), Dr. Kassim Muhammad Kassim, ya bukaci ‘yan Najeriya da su rungumi aure tsakanin kabilu, yana mai cewa hakan na ƙarfafa ɗaukaka da haɗin kai a ƙasa ta hanyar haɗin al’adun juna.
Dr. Kassim ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi baƙuncin matasa masu yi wa ƙasa hidima (NYSC) na Batch B, Stream 2, shekarar 2024/2025 waɗanda suke yin aikin su tare da hukumar.
Ya ce, auren tsakanin kabilu daban-daban yana ba ma’aurata damar rayuwa cikin zaman lafiya da fahimtar juna. Ya ƙara da cewa:
“Duk wanda ya yi aure a Jihar Nasarawa, musamman cikin mazauna jihar, hukumar NSUBEB za ta ba shi **aikin dindindin kai tsaye (automatic appointment).”
Ya kuma ja hankalin ‘yan NYSC da su dauki aikin shekarar su daya a matsayin dama ta bayar da gudunmawa ga ƙasar su – Najeriya kafin su je neman aiki ko wata dama a wani wuri.
“Mun sani kasuwar aiki cike take, ba kowa ke samun aiki ba. Don haka ina shawartar ku da ku koya sana’o’in hannu ko kanana, don samun hanyar rayuwa idan aikin gwamnati bai samu ba,” inji Dr. Kassim.
A nata jawabin, Amina Dahiru Adamu, shugabar tawagar ‘yan NYSC, ta ce sun kawo ziyara ne domin taya Dr. Kassim murna bisa nadin da aka masa a matsayin Shugaban NSUBEB daga Gwamna Abdullahi Sule, da kuma nuna godiyarsu ga ma’aikatan hukumar bisa irin hadin kan da suka samu cikin shekara guda da suka shafe suna yi wa hukumar aiki.
Ta kuma bayyana cewa lokacin su na aikin NYSC zai ƙare ƙarshen wannan wata, tare da alkawarin cewa za su aiwatar da duk abin da suka koya a lokacin aikin su.
A ƙarshe, sun mika kyaututtuka ga Shugaban hukumar a matsayin girmamawa.
