Fitaccen ɗan gwagwarmayar Indiya, Sonam Wangchuk, ya kawo ƙarshen yajin cin abincin da ya shafe kwanaki 26 yana yi domin neman murabus ɗin Ministan Ilimi, Dharmendra Pradhan, sakamakon yawaitar satar takardun jarabawa a ƙasar.
Wangchuk mai shekaru 59 ya sanar da kawo ƙarshen yajin cin abincin ne ta shafinsa na X, inda ya ce ya ɗauki matakin ne bayan doguwar tattaunawa da aka yi da kuma kauce wa yiwuwar tashin hankali a ƙasar.
Ya ce zai yi ƙarin bayani kan dalilan da suka sa ya dakatar da yajin cin abincin a wani bidiyo da zai fitar nan gaba.
Wangchuk ya fara yajin cin abincin ne tun ranar 28 ga Yuni, domin nuna goyon baya ga matasan jam’iyyar Cockroach Janta Party (CJP), waɗanda ke neman ministan ilimin ya sauka saboda satar takardun jarabawar shiga kwalejin koyon aikin likitanci, lamarin da ya tilasta wa miliyoyin ɗalibai sake rubuta jarabawar.
Sanarwar tasa ta zo ne jim kaɗan bayan Firaministan Indiya, Narendra Modi, ya fitar da saƙo inda ya yi alƙawarin ɗaukar tsauraran matakai domin dakile satar takardun jarabawa.
Modi ya ce gwamnati za ta hanzarta gurfanar da masu hannu a wannan laifi a gaban kotu, tare da bayyana cewa majalisar ministoci za ta tattauna batun domin samar da mafita mai ɗorewa.
Firaministan ya bayyana satar takardun jarabawa a matsayin babban abin takaici ga ɗaruruwan dubban ɗalibai, sai dai bai ambaci sunan Ministan Ilimi, Dharmendra Pradhan, a jawabinsa ba.
