Akalla sojoji 16 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu 23 suka jikkata sakamakon wani hari da ake zargin ‘yan ta’adda ne suka kai kan rundunar sojojin Jamhuriyar Nijar a yankin Tera da ke jihar Tillaberi.
Kamfanin dillancin labaran gwamnatin Nijar (ANP) ya bayyana cewa harin ya faru ne ranar Juma’a, 17 ga Yuli, 2026, a yankin da ke kusa da iyakokin Mali da Burkina Faso.
Rahoton ya ce cikin sojojin da suka jikkata, tara na cikin mawuyacin hali. Haka kuma, jami’an tsaro sun ce sun kashe ‘yan ta’adda 15 yayin artabun.
ANP ta kara da cewa dakarun tsaro na ci gaba da gudanar da bincike, sintiri da kuma farautar maharan domin tabbatar da tsaron yankin.
Jamhuriyar Nijar ta shafe sama da shekaru goma tana fama da hare-haren kungiyoyin masu ikirarin jihadi masu alaka da Al-Qaeda da kuma ISIS. Duk da juyin mulkin da sojoji suka yi a shekarar 2023, matsalar tsaro na ci gaba da kasancewa babban kalubale a kasar.
