Shirin da magajin garin Yawata a yammacin Japan, Shoko Kawata, mai shekara 35, ta yi na tafiya hutun haihuwa ya tayar da muhawara a fadin kasar kan ko ya dace zababbun jami’an gwamnati su dakatar da aikinsu domin haihuwa.
Kawata, wadda ke jiran haihuwar danta na farko a tsakiyar watan Satumba, za ta zama magajin gari ta farko a tarihin Japan da za ta tafi hutun haihuwa. Matakin nata ya samu yabo daga wasu, yayin da wasu kuma suka soki wannan shawara.
Ta bayyana cewa ba ta yi tsammanin sanarwar tata za ta jawo irin wannan martani ba.
Garin Yawata, da ke kudancin Kyoto, ba shi da wata doka da ke bai wa zababbun jami’an gwamnati damar tafiya hutun haihuwa. Saboda haka, Kawata ta mika ragamar tafiyar da harkokin ofishinta ga mataimakinta, Shigeto Nose, wanda zai rike mukamin na wucin gadi yayin da take hutu.
Kawata ta sanar tun a watan Mayu cewa za ta dakatar da ayyukan ofis na tsawon watanni hudu, watanni biyu kafin haihuwa da kuma watanni biyu bayan haihuwa. Duk da haka, ta ce za ta ci gaba da shiga manyan shawarwari ta hanyar tarurrukan yanar gizo da mataimakinta.
Wasu sun yabawa matakin nata, suna cewa hakan zai karfafa gwiwar mata su shiga siyasa tare da nuna cewa ana iya hada aikin gwamnati da kula da iyali. Sai dai masu suka sun ce zababbun shugabanni ya kamata su fifita ayyukan jama’a, inda wasu suka bukaci ta yi murabus ko kuma a rage albashinta yayin hutun.
Kawata ta yi watsi da wadannan suka, tana mai cewa bai kamata mata su zabi tsakanin aikin gwamnati da zama uwa ba.
Ta ce idan ana sukar ‘yan siyasa saboda tafiya hutun haihuwa, hakan na nufin ana hana mata masu shekaru tsakanin 20 zuwa 40 damar shiga siyasa.
Kawata ta kafa tarihi a shekarar 2023 lokacin da ta zama magajin gari mace mafi karancin shekaru a Japan tana da shekara 33. Ta kammala karatu a Jami’ar Kyoto a fannin tattalin arziki.
Kididdigar gwamnati ta nuna cewa mata na wakiltar kusan kashi hudu cikin dari kacal na shugabannin kananan hukumomi 1,720 da ke Japan, lamarin da ke nuna karancin wakilcin mata a siyasar kasar.
A cewar wani bincike da Ofishin Majalisar Ministocin Japan ya gudanar a shekarar 2025, daukar ciki, son zuciya kan jinsi da cin zarafi na daga cikin manyan kalubalen da ke hana mata shiga siyasa.
Mataimakin magajin garin, Shigeto Nose, wanda zai jagoranci gudanar da harkokin garin yayin hutun Kawata, ya ce lokaci ya sauya matuka idan aka kwatanta da lokacin da yake rainon yaransa, yana mai bayyana cewa yanzu yana farin ciki ganin matasa na raba nauyin kula da yara tsakanin ma’aurata.
Kawata ta bayyana fatan cewa matakin da ta dauka zai taimaka wajen gina al’umma inda mata za su iya hada shugabanci da zama uwa ba tare da an tilasta musu zabi tsakanin aiki da iyali ba.
