Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) reshen Jihar Osun ta yabawa Rundunar ‘Yan Sandan jihar bisa dakile wani yunkurin da ake zargin an yi na kashe Darakta Janar na Kwamitin Yakin Neman Zaben Gwamnanta, Wole Oke.
A ranar Alhamis ne rundunar ‘yan sandan ta gabatar da wani DJ mai suna Olalekan Oriyomi tare da wasu mutane biyu, Ayotunde Ikupolati mai shekara 44 da Femi Fakinleye mai shekara 31, bisa zargin yunkurin kashe Oke a garin Ipetu Ijesa.
‘Yan sanda sun kuma ce sun kwato bindigar Beretta dauke da harsasai guda hudu daga hannun daya daga cikin wadanda ake zargin.
A cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na APC a Osun, Kola Olabisi, ya sanya wa hannu, jam’iyyar ta yaba da kokarin ‘yan sanda na dakile aikata laifuka da tabbatar da tsaro a jihar.
Jam’iyyar ta ce da a ce wadanda ake zargin sun yi nasara, da jihar za ta fada cikin wani sabon yanayi na jimami, tana mai bayyana cikakken amincewarta cewa ‘yan sanda za su gudanar da bincike mai zurfi domin gano tare da gurfanar da duk wanda ke da hannu a lamarin.
APC ta kuma bayyana damuwarta kan rashin jin Allah wadai daga Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, da kuma shugaban jam’iyyar Accord a jihar, Victor Akande, kwanaki bayan faruwar lamarin.
Jam’iyyar ta bukaci rundunar ‘yan sanda da ta ci gaba da tsaurara bincike tare da kamo dukkan wadanda ake zargin suna da hannu a shirin, ciki har da manyan mutane da ake zargin wadanda aka kama suka ambata yayin bincike.
A karshe, APC ta bukaci magoya bayanta su ci gaba da yakin neman zaben dan takararta na gwamna, Asiwaju Oyebamiji, cikin lumana da bin doka, tana mai bayyana cewa tana da yakinin samun nasara a zaben gwamnan jihar da za a gudanar ranar 15 ga Agusta, 2026.
