Dan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Sagbama/Ekeremor ta Jihar Bayelsa, Frederick Agbedi, ya zama sabon Jagoran ‘Yan Adawa (Minority Leader) a Majalisar Wakilai ta Tarayya.
Nadin Agbedi ya biyo bayan murabus din tsohon Jagoran ‘Yan Adawa, Kingsley Chinda na Jihar Rivers, wanda ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC mai mulki.
An sanar da nadin ne a zaman majalisar na ranar Alhamis bayan kungiyar ‘yan adawa ta aikewa Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, wasika mai kunshe da sunayen sabbin shugabannin da aka amince da su ta hanyar matsaya guda.
Yayin karanta wasikar, Abbas ya bayyana cewa kungiyar ‘yan adawa ta zabi Agbedi a matsayin Jagoran ‘Yan Adawa, yayin da aka zabi Hon. Mansur Soro na jam’iyyar APM a matsayin Minority Whip, sannan Hon. Abdussamad Dasuki na jam’iyyar ADC ya zama Mataimakin Jagoran ‘Yan Adawa.
Da wannan nadin, Agbedi zai jagoranci hada kan ‘yan adawa a majalisar tare da bayyana matsayinsu kan muhimman dokoki da batutuwan da ke gaban zauren majalisar.
Agbedi na daga cikin tsofaffin ‘yan majalisar da suka fi dadewa a Majalisar Wakilai, inda yake wakiltar mazabarsa tun daga shekarar 2011.
Masu sa ido kan harkokin siyasa na ganin nadin nasa zai taimaka wajen karfafa murya da hadin kan ‘yan adawa musamman a lokacin da ake fuskantar sauye-sauyen siyasa da sauya sheka gabanin babban zaben shekarar 2027.
Bayan sanar da nadin, Kakakin Majalisar, Tajudeen Abbas, ya taya sabbin shugabannin murna tare da tabbatar musu da hadin kan shugabancin majalisar domin cimma manufofin majalisa ta 10.
Sabbin nade-naden sun kawo karshen makwanni na rashin tabbas a bangaren ‘yan adawa bayan sauya shekar Kingsley Chinda, lamarin da ya haifar da gibin shugabanci a majalisar.
Ana sa ran sabbin shugabannin za su fuskanci kalubalen hada kan ‘yan majalisa daga jam’iyyun adawa daban-daban tare da gudanar da sahihin sa ido kan ayyukan gwamnati da majalisar da APC ke da rinjaye a cikinta.
