Gwamnatin Tarayya ta amince da biyan kudaden kwangila ga kwangiloli 1,240 da ke aiki da ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati (MDAs), inda aka ba da fifiko ga wadanda ake bin su kasa da Naira miliyan 100.
A cikin wata sanarwa da Babbar Mataimakiya ta Musamman kan Sadarwa ga Ministan Kudi, Mary-Ann Duke, ta fitar a ranar Litinin, ta ce an dauki matakin ne bayan kammala tantancewa da tabbatar da sahihancin basussukan da gwamnati ke bi.
Ta bayyana cewa wannan mataki zai taimaka wajen samar da kudaden aiki ga kamfanoni da ‘yan kwangila a fadin kasar tare da nuna kudirin gwamnati na cika alkawurranta na biyan hakkokin masu kwangila.
Ma’aikatar Kudi ta ce biyan kudaden zai rage wa kamfanonin cikin gida da kanana da matsakaitan masana’antu radadin matsin tattalin arziki, tare da ba su damar komawa wuraren ayyuka, biyan ma’aikata da kuma warware bashin masu samar musu da kayayyaki.
A cewar ma’aikatar, an riga an tantance tare da fara biyan sama da Naira biliyan 700 na basussukan da ake bin ‘yan kwangilar cikin gida a watannin baya-bayan nan.
Sanarwar ta kara da cewa a watan Mayu kadai, an gudanar da mu’amaloli da suka kai kusan Naira biliyan 436.6, lamarin da ke nuna karuwar saurin biyan kudaden da gwamnati ke bi.
Gwamnatin ta bayyana cewa ba da fifiko ga kananan ‘yan kwangila zai taimaka wajen bunkasa ayyukan tattalin arziki a sassa daban-daban na kasar, kare ayyukan yi da kuma tabbatar da kammala ayyukan ci gaba da ake gudanarwa.
Haka kuma, ana sa ran matakin zai kara wa ‘yan kwangila, masu samar da kayayyaki da masu ba da hidima ga gwamnati kwarin gwiwa wajen ci gaba da gudanar da ayyukansu.
A watan Janairu, wasu ‘yan kwangilar cikin gida sun hana Karamin Ministan Kudi, Doris Uzoka-Anite, shiga ma’aikatar saboda jinkirin biyan basussukan da ake binsu. Bayan watanni shida, Majalisar Dattawa ta kafa kwamitin da zai tattauna da Ma’aikatar Kudi kan bashin da ake bin ‘yan kwangila.
