Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya bayyana cewa wasu ‘yan Najeriya na taimaka wa ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga ta hanyar ba su abinci, ruwa, bayanan sirri da sauran kayan tallafi, lamarin da ke sa yaki da rashin tsaro ya zama mai wahala.
Musa ya bayyana hakan ne yayin wani taron lacca na musamman da aka shirya domin bikin Ranar Dimokuradiyya a Legas, inda ya ce matsalar ta’addanci, tada kayar baya da ayyukan ‘yan bindiga ba za su kare ba sai jama’a sun daina ba masu aikata laifuka goyon baya.
A cewarsa, nasarar da ake nema a yakin da ake yi da ‘yan ta’adda ta ta’allaka ne ga hadin kai da goyon bayan al’umma.
“‘Yan bindiga da ‘yan ta’adda suna rayuwa ne a tsakanin mutane. Akwai wadanda ke ba su abinci, ruwa, bayanai da sauran abubuwan da ke taimaka musu ci gaba da aikata laifuka,” in ji shi.
Ministan ya ce duk da kokarin da jami’an tsaro ke yi, ba za a samu cikakkiyar nasara ba idan jama’a ba su bayar da hadin kai wajen gano da tona asirin masu aikata laifuka ba.
Ya kuma bayyana cewa yakin zamani ya bambanta da na baya, domin a yanzu makiya kan kasance cikin al’umma ba tare da an san su ba.
Musa ya yaba wa ‘yan Najeriya bisa jajircewarsu wajen goyon bayan kokarin dawo da zaman lafiya, tare da yin kira ga kowa da kowa da ya hada kai domin kawo karshen matsalar rashin tsaro a fadin kasar nan.
Ya kara da cewa masu aikata laifuka kan yi anfani da rabuwar kai da rashin hadin kai tsakanin jama’a domin cimma mugayen manufofinsu, don haka ya bukaci ‘yan Najeriya su kasance tsintsiya madaurinki daya.
