Kocin Napoli, Antonio Conte, ya bayyana cewa kocin Manchester City, Pep Guardiola, shi ne wanda ya fi dacewa da aikin horas da tawagar ƙasar Italy.
Conte ya bayyana hakan ne yayin da ake ci gaba da raɗe-raɗin cewa ana danganta shi da kujerar kocin ƙungiyar ƙwallon ƙafar ƙasar Italy.
Sai dai ya ce babu wata tattaunawa ko yarjejeniya tsakaninsa da Hukumar Ƙwallon Ƙafar Italy kan aikin.
“A yanzu babu komai tsakaninmu da Hukumar Ƙwallon Ƙafar Italy dangane da aikin koci. Babu wata magana har yanzu. Nan gaba ne za a gani,” in ji shi.
Ya kuma bayyana cewa har yanzu ma ba a tabbatar da shugabancin hukumar ba, yana mai tambayar ko Italy na da shirin ɗaukar babban koci mai tsada.
Conte ya ce idan za a tambaye shi wanda ya dace da aikin, zai zaɓi Guardiola, amma ya nuna shakku kan ko hukumar za ta iya biyan kuɗin ɗaukar irin wannan babban koci.
“Ina jin ana maganar Pep Guardiola. Idan zan bada shawara, zan ce Pep ne. Amma tambayar ita ce, suna da kuɗin da za su iya ɗaukar sa?” in ji Conte.
Rahotanni dai na nuna cewa Conte na dab da barin Napoli a ƙarshen kakar wasa, lamarin da ya ƙara ƙarfafa jita-jitar alaƙarsa da kujerar horas da tawagar Italy.
