Jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) ta kafa Kwamitin Zaɓe na Ƙasa mai mambobi 20 a matsayin wani ɓangare na shirye-shiryenta na fidda gwani na kujerun gwamna da Majalisar Tarayya gabanin zaɓen 2027.
Jam’iyyar ta ce matakin na cikin manufarta ta tabbatar da gaskiya, sahihanci, da ingantaccen tsarin dimokiraɗiyya a cikin harkokin zaɓen ‘yan takara.
A cikin wata sanarwa da Sakataren Ƙasa, Hon. (Barr.) Ikenna Morgan Enekweizu, ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa an amince da kafa kwamitin ne bisa shawarar Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NWC) tare da amincewar jagorancin jam’iyya.
Kwamitin zai duba, tantance tare da nazarin rahotanni da shawarwarin da Kwamitin Tantance ‘Yan Takara ya gabatar, sannan ya yanke hukunci kan sakamakon tantancewar ‘yan takara da ke neman tikitin jam’iyyar.
Fitattun mutane da aka nada sun haɗa da Buba Galadima, Farfesa Udenta Udenta da Yunusa Tanko, tare da sauran mambobi da suka fito daga fannoni daban-daban na siyasa da ilimi.
Shugaban kwamitin shi ne Sanata Cleopas Moses Zuwoghe, yayin da Barr. Ikenna Morgan Enekweizu zai riƙe matsayin sakatare.
Jam’iyyar ta yi kira ga ‘yan takara da masu ruwa da tsaki da su ba da haɗin kai, tana mai cewa an tsara wa kwamitin lokaci ƙanƙani don kammala aikinsa cikin gaggawa da inganci.
NDC ta ce manufar tsarin ita ce ƙarfafa tattaunawa da cimma matsaya ɗaya (consensus building) domin samar da ‘yan takara masu karɓuwa ga jama’a.
Ta ƙara da cewa duk wanda zai tsaya takara dole ne ya wuce tantancewar Kwamitin Screening da kuma Kwamitin Selection kafin ya cancanci sayen fom.
Idan kuma ba a cimma matsaya ɗaya ba, za a gudanar da zaɓen fidda gwani kai tsaye tsakanin 28 zuwa 30 ga Mayu, 2026.
An shirya kaddamar da kwamitin a hukumance a ranar 25 ga Mayu, 2026, inda zai fara aikinsa nan take.
