Shugaban Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Najeriya (NDLEA), Buba Marwa, ya yi gargaɗi ga ‘yan gungun dillalan miyagun ƙwayoyi da ke aiki a Yammacin Afirka cewa sabuwar haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da Ghana za ta ƙara matsa musu lamba sosai.
Marwa ya yi wannan gargadi ne a Abuja a ranar Talata yayin da ya karɓi tawagar Hukumar Narcotics Control Commission ta Ghana, wadda ke karkashin jagorancin Darakta-Janar, Maxwell Mantey.
Ya ce haɗin gwiwar za ta taimaka wajen musayar bayanan sirri, dabarun aiki, binciken dijital, da horar da jami’ai domin inganta yaki da miyagun ƙwayoyi a yankin.
Marwa ya ce: “Bari wannan ziyara ta zama gargaɗi ga duk masu son lalata al’umma da miyagun ƙwayoyi: Najeriya da Ghana sun haɗa kai.”
Ya bayyana cewa wannan haɗin gwiwa zai ƙara ƙarfin aiki da hadin kai wajen yaƙi da masu safarar miyagun ƙwayoyi da laifukan da ke da alaƙa da su kamar wanke kuɗaɗe.
A nasa jawabin, shugaban tawagar Ghana, Maxwell Mantey, ya yaba da rawar da Najeriya ke takawa a yaki da miyagun ƙwayoyi a yankin, yana mai cewa haɗin gwiwar na da muhimmanci saboda barazanar da ke ƙaruwa.
Ya ce safarar miyagun ƙwayoyi na ƙara rikitarwa, inda masu laifi ke amfani da sabbin hanyoyi da fasaha wajen aikata laifi.
Ya ƙara da cewa ba zai yiwu ƙasa ɗaya ta magance wannan matsala ita kaɗai ba, don haka haɗin kai ya zama wajibi.
