Attajirin dan kasuwa, Femi Otedola, ya karyata rahotannin da ke yawo cewa ya taimaka wajen daukar nauyin gina matatar man Dangote, yana mai bayyana zarge-zargen a matsayin karya da yaudara.
A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin, Otedola ya ce bai saka ko sisi guda ba a aikin matatar.
“Rahotannin da ke cewa Femi Otedola ya dauki nauyin matatar Dangote gaba daya karya ne. Bai zuba ko kobo daya ba, ko dala daya, ko naira daya,” in ji shi.
Ya bayyana cewa gaskiyar lamarin ita ce yana neman damar shiga tayin hannun jari na kamfanin idan aka bude shi ga jama’a.
Otedola ya kara da cewa Aliko Dangote bai taba neman tallafin kudi daga gare shi ko wasu manyan ‘yan kasuwa irin su Tony Elumelu da Mike Adenuga ba.
“Dangote Group tsari ne mai karfi wanda ya kware wajen tara jari cikin tsarin kasuwanci na zamani,” ya bayyana.
Ya ce yada irin wadannan rahotanni wata hanya ce ta haddasa rikici da rarrabuwar kawuna tsakanin manyan ‘yan kasuwar Najeriya.
“Wannan wata mummunar manufa ce ta kirkirar rikici a tsakanin shugabannin kamfanoni masu daraja a Najeriya,” in ji Otedola.
Shi ma Kamfanin Dangote Group ya fitar da sanarwa yana mai karyata rade-radin cewa an gina matatar ne da bashin sirri daga abokai ko wasu attajirai.
Kamfanin ya bayyana cewa tsarin samar da kudaden aikin ya bi hanyoyin kasuwanci na hukuma kuma babu wata matsala tsakanin Dangote da Tony Elumelu.
Dangote Group ya gargadi masu yada labaran karya da su daina yada bayanan da ka iya rage martabar bangaren kasuwanci na Najeriya.
