Tsohon dan takarar shugaban kasa kuma attajirin bangaren makamashi, Dakta Gbenga Olawepo-Hashim, ya yi kakkausar suka kan mummunan harin da ‘yan bindiga suka kai wa masu ibada a Cocin Christ Apostolic Church (CAC) No. 2 da ke Eda Oniyo, karamar hukumar Ilejemeje ta jihar Ekiti, inda ya bayyana lamarin a matsayin abin firgici da matukar tayar da hankali.
Rahotanni sun bayyana cewa kimanin ‘yan bindiga bakwai dauke da muggan makamai sun kutsa cikin taron farfadowa da aka gudanar da misalin karfe 7:30 na dare, inda suka bude wuta kan masu ibada, suka kashe faston da aka gayyata sannan suka yi awon gaba da akalla mutum 13.
Shaidun gani da ido sun ce harin ya dauki kusan mintuna 40, lamarin da ya jefa al’ummar yankin cikin firgici yayin da mazauna garin suka rika gudun ceton rayukansu.
Da yake mayar da martani, Olawepo-Hashim ya nuna matukar alhini kan asarar rayuka da kuma sace bayin Allah da ba su ji ba ba su gani ba.
“Ina mika sakon ta’aziyyata ga iyalan faston da aka kashe, cocin, da daukacin al’ummar Eda Oniyo da kewaye. Haka kuma ina addu’ar Allah ya kubutar da wadanda aka sace cikin koshin lafiya,” in ji shi.
Ya kuma nuna damuwa kan rahotannin da ke cewa jami’an tsaro sun dauki lokaci kafin su isa wajen duk da kiran neman dauki da aka yi, yana mai cewa da an dauki mataki cikin gaggawa, da barnar ba ta kai haka ba.
“Ba za mu ci gaba da barin al’ummominmu cikin tsoron miyagu ba. Wuraren ibada dole su kasance wuraren zaman lafiya, ba filayen tashin hankali ba,” ya bayyana.
Yayin da ya yaba da kokarin jami’an tsaro da ke ci gaba da bincike a dazuka da kewaye domin ceto wadanda aka sace, ya bukaci a samar da ingantaccen tsarin tsaro na bai daya wanda zai fi mayar da hankali kan bayanan sirri da daukar matakin gaggawa.
Olawepo-Hashim ya bukaci hukumomin tsaro su kara kaimi wajen tabbatar da ceto wadanda aka yi garkuwa da su tare da kamo masu hannu a harin domin gurfanar da su gaban kuliya.
Haka kuma ya roki gwamnatocin tarayya, jihohi da kananan hukumomi da su kara karfafa tsare-tsaren tsaro a matakin al’umma, inganta hanyoyin daukar matakin gaggawa, tare da dawo da amincewar jama’a kan kariyar rayuka da dukiyoyi.
Wannan hari ya sake jawo hankalin jama’a kan matsalar rashin tsaro da ke ci gaba da addabar al’ummomin karkara da wuraren ibada a sassan Najeriya.
