Yerima Shettima, daya daga cikin masu neman takarar kujerar Sanata a mazabar Kaduna ta Tsakiya, ya karbi fom din tsayawa takara na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) domin zaben shekarar 2027.
An tattara fom din ne a ranar Talata ta hannun wakilansa, Danjuma Paul da Barrister Onus Eugene, wanda hakan ke nuna cewa ya shiga takarar a hukumance yayin da harkokin siyasa ke kara daukar zafi a jihar Kaduna.
Bayan kammala karbar fom din, Shettima ya bayyana cewa wannan mataki na nufin kawar da shakku kan ko yana da niyyar tsayawa takara, yana mai jaddada cewa burinsa shi ne samar da ingantaccen wakilci mai amfani ga al’umma.
Ya tunatar da cewa kwanan nan ya jagoranci dimbin magoya bayansa wajen ziyarar ayyana takara a ofishin shugabancin APC a Kaduna, inda ya sanar da aniyarsa a hukumance.
Shettima ya ce ya shirya tsayawa takara a zaben fidda gwani na jam’iyya, yana mai musanta rade-radin cewa za a iya samar da dan takara guda ta hanyar sulhu (consensus).
A cewarsa, mazabar Kaduna ta Tsakiya na bukatar wakilci nagari da ingantaccen shugabanci, yana mai cewa yana da kwarewa, gaskiya da karbuwa a tsakanin jama’a da za su ba shi damar yin aiki yadda ya kamata.
Shettima, wanda tsohon shugaban kungiyar Arewa Youth Consultative Forum (AYCF) ne kuma mai kafa Northern Stakeholders Consultative Initiative (NSCI), ya ce gogewarsa a fannin fafutukar matasa ta kara masa kwarewa da kusanci da al’umma, tare da fahimtar matsalolinsu.
A bangaren goyon baya kuma, shugaban Capacity Movement, Shehu Sani Sado, ya bayyana Shettima a matsayin dan takara mai karfi, yana mai cewa yanayin siyasar yanzu na iya taimaka masa samun nasara.
