Gwamnatin Jihar Osun ta sauke Oba Gbenga Oloyede daga sarautar Apetumodu na Ipetumodu da ke karamar hukumar Ife North, tare da ayyana kujerar a matsayin babu mai rike da ita nan take.
A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labarai na jihar, Kolapo Alimi, ya fitar ranar Litinin, gwamnatin ta ce matakin ya biyo bayan shawarwari, nazarin doka da kuma amincewar Majalisar Zartarwa ta jihar.
Sanarwar ta ce an dauki matakin ne bisa Dokar Sarakunan Jihar Osun (Chiefs Law) da sauran dokokin da ke jagorantar al’amuran sarauta a jihar.
Gwamnatin ta kuma janye sandar sarauta da dukkanin ikon da aka bai wa Oba Oloyede, tare da bayyana cewa za a sanar da matakan da za a bi wajen nada sabon sarki nan gaba.
An kuma umarci jami’an tsaro da su tabbatar da zaman lafiya a yankin, yayin da aka bukaci al’umma da su kwantar da hankali tare da bin doka.
Wannan mataki na zuwa ne bayan an samu rahoton cewa Oba Oloyede, wanda ke da zama biyu (Nigeria da Amurka), an yanke masa hukuncin daurin shekaru hudu a gidan yari a Amurka a watan Agustan 2025.
An same shi da laifin jagorantar wata badakalar satar kudaden tallafin COVID-19 da aka ware domin taimakawa kananan ‘yan kasuwa.
Hukumar shari’a ta Amurka ta kuma umarce shi da ya biya diyyar dala miliyan 4.4, tare da kwace masa dukiyoyi da aka samu daga haramtacciyar hanya.
Tun bayan hukuncin, rikici ya kunno kai a Ipetumodu, inda wasu bangarori ke sabani kan ko a jira dawowarsa ko kuma a nada sabon sarki.
Rikicin ya kuma jawo rokon wasu gidajen sarauta biyu da masu nada sarakuna a yankin ga gwamnatin jihar da ta gaggauta cike gurbin kujerar.
