Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ya bayyana cikin barkwanci yadda wani abin mamaki ya sa ya daina shan giya gaba ɗaya.
A wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta ranar Talata, Osinbajo ya ce duk da kasancewarsa fasto, a baya yana shan jan giya da kuma giya lokaci zuwa lokaci.
“Ina son jan giya lokaci-lokaci, sannan kuma ina shan beer,” in ji shi.
Sai dai ya ce wata rana yayin da yake aiki da Hukumar Majalisar Dinkin Duniya a bangaren shari’a a Mogadishu, Somalia, wani lamari ya sauya rayuwarsa.
Osinbajo ya ce bayan ya gama wa’azi a cocin fellowship ranar Lahadi, yana hanyarsa ta zuwa siyan gwangwanin giya biyu na Heineken domin komawa dakinsa ya karanta Littafi Mai Tsarki.
A lokacin da ya shiga wani gidan cin abinci a harabar UN, sai ya tarar da wasu abokan aikinsa daga kasashe daban-daban suna shan giya.
Da suka gan shi, sai suka boye giyoyinsu saboda girmamawa.
Ya ce ya tambayi wani abokinsa dan kasar Denmark dalilin da ya sa yake boye whiskey dinsa, sai mutumin ya amsa da cewa:
“Kai fasto ne, ba za mu iya shan giya a gabanka ba.”
Osinbajo ya ce wannan magana ta taba zuciyarsa sosai, kuma ya dauke ta a matsayin sako daga Allah.
Daga nan ne ya fahimci ma’anar ayar Littafi Mai Tsarki da ke cewa:
“Komai halal ne a gare ni, amma ba komai ne ya dace ba.”
Tun daga wannan rana, ya ce bai sake shan giya ba.
Labarin ya jawo martani daban-daban a shafukan sada zumunta, inda wasu suka bayyana shi a matsayin darasi mai ma’ana, yayin da wasu suka dauke shi cikin raha da nishadi.
