Karamin Ministan Albarkatun Man Fetur (Gas), Rt. Hon. Ekperikpe Ekpo, ya yaba wa kamfanin Southfield Petroleum Limited da hukumar NCDMB bisa rawar da suke takawa wajen bunƙasa harkar gas a Najeriya ta hanyar zuba jari a manyan ayyuka.
Ya bayyana hakan ne a wajen bikin kaddamar da aikin gina tashar sarrafa gas mai karfin MMSCFD 200 ta Southfield Petroleum a Utorogu, jihar Delta.
Ekpo, wanda Daraktan Gas na Ma’aikatar Albarkatun Man Fetur, Mista Elisha Benjamin Dan-Asabe, ya wakilta, ya ce aikin ya yi daidai da burin gwamnatin tarayya na amfani da gas wajen bunkasa tattalin arziki da samar da makamashi mai dorewa.
Ya ce aikin zai taimaka wajen kara samar da isasshen gas da kuma inganta samar da wutar lantarki a fadin kasar nan, tare da tallafa wa masana’antu.
Haka kuma ya yaba wa NCDMB bisa kokarinta wajen inganta shigar ‘yan Najeriya a harkar man fetur da gas, musamman a yankin Niger Delta.
A cewarsa, hadin gwiwa tsakanin gwamnati da masu zuba jari da al’umma zai taimaka wajen tabbatar da nasarar ayyukan makamashi da samar da ayyukan yi.
