Wanda ya kafa Living Faith Church Worldwide (Winners Chapel), Bishop David Oyedepo, ya bayyana cewa babu wata gwamnati a duniya da za ta iya tabbatar da zaman lafiya na hakika, yana mai kira ga muminai da su dogara ga Allah a matsayin tushen zaman lafiya na gaskiya.
Oyedepo ya bayyana hakan ne yayin bikin kaddamar da sabon wurin ibada na Master’s Place International Church mai suna Dreamland, Master’s City, a Warri, Jihar Delta.
Da yake wa’azi kan taken “Me Ya Sa Ake Keɓe Wuraren Ibada?”, Oyedepo ya ce ana keɓe majami’u ne domin su na Allah, wanda shi ne mamallaki kuma mai gina cocinsa.
Ya ce:
“Allah ne mamallaki kuma mai gina cocinsa. Daukakar Allah za ta cika wannan gida, kuma zai zama gidan ceto da wurin zamansa.”
Malamin ya kara da cewa zaman lafiya na gaskiya ba ya fitowa daga gwamnati ko tsarin duniya.
“Babu wata gwamnati a duniya da za ta iya ba ka zaman lafiya, kuma ba za ka same shi a kasuwa ba. Allah ne kadai ke ba da zaman lafiya.”
A yayin taron, an kuma sake naɗa Fasto Korede Komaiya da matarsa Fasto Esther Komaiya domin ci gaba da jagorantar cocin, inda Bishop Oyedepo ya yi musu addu’o’i tare da yi musu fatan alheri a sabon matakin hidimarsu.
Oyedepo ya taya cocin da mambobinta murnar kammala ginin sabon wurin ibadar, yana mai cewa mafi alheri yana gaba.
Taron ya zo daidai da International Founders Conference 2026, inda dubban masu ibada da fitattun shugabannin Kirista daga Najeriya da sauran kasashe suka halarta.
