Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana rashin jin dadinsa kan gazawar tawagar Super Eagles ta Najeriya wajen samun tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA 2026.
Wike ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin kaddamar da titin Kuje-Gwagwalada a Abuja, inda tsohon kyaftin din Super Eagles, Joseph Yobo, ya halarci taron.
Ministan ya ce har yanzu ‘yan Najeriya da dama suna cikin takaici saboda rashin ganin kasarsu a gasar kofin duniya duk da cewa an fadada gasar zuwa kasashe 48.
Ya ce yana mamakin yadda wasu kasashen da ba su da tarihin kwallon kafa irin na Najeriya suka samu damar halartar gasar, yayin da Najeriya ta kasa samun tikitin shiga.
“Ta hannunka nake son a sanar da ‘yan wasan Super Eagles cewa ba mu ji dadi ba. Wasu na tafa musu, amma dole ne wani ya gaya musu gaskiya,” in ji Wike.
Ya kara da cewa yana kallon wasannin kofin duniya na tsawon lokaci yana ganin kasashe da bai taba jin sunansu ba suna fafatawa, alhali Najeriya ba ta cikin gasar.
Wike ya nuna cewa akwai ‘yan wasan Najeriya da dama da ke taka leda a manyan kungiyoyi a duniya, amma duk da haka kasar ta kasa samun gurbi a gasar.
Da yake magana kai tsaye da Joseph Yobo, ministan ya ce, “Yobo, ka je ka fada musu cewa ba mu ji dadi ba.”
Najeriya dai ta kasa samun gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026 bayan ta gaza a wasannin neman tikitin shiga gasar, duk da karin yawan kasashen da za su halarta.
Daga baya kuma tawagar ta fice daga fafatawar neman tikitin ne bayan shan kashi a bugun daga kai sai mai tsaron gida a hannun Congo.
Kalaman Wike sun sake tayar da muhawara tsakanin magoya bayan kwallon kafa a Najeriya kan makomar Super Eagles da kuma matakan da ya kamata a dauka domin dawo da martabar tawagar.
