Dan majalisar wakilai kuma Darakta Janar na Kwamitin Yakin Neman Zaben Gwamnan Jihar Osun, Oluwole Oke, ya musanta zargin da ke alakanta shi da jam’iyyar APC da mutuwar wani mamba na jam’iyyar Accord, Ajayi Aderogba, wanda aka fi sani da Rogba.
An harbe Aderogba har lahira ne a ranar Talata a garin Esa Oke da ke karamar hukumar Obokun ta Jihar Osun yayin shirye-shiryen wani taron siyasa na goyon bayan wa’adin mulki na biyu na Gwamna Ademola Adeleke.
Mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben Adeleke, Pelumi Olajengbesi, ya yi zargin cewa Oluwole Oke ne ke da hannu a harin da ya yi sanadin mutuwar Rogba.
Sai dai a wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Tunde Omolebi-Sunday, ya fitar a ranar Laraba, Oke ya yi watsi da zargin tare da bayyana shi a matsayin mara tushe kuma mai yaudara.
Ya bayyana kaduwarsa da alhininsa kan mutuwar marigayin tare da mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalansa, abokansa da al’ummar Esa Oke.
Oke ya kuma soki wadanda suka yi zargin kafin hukumomin tsaro su kammala bincike, yana mai cewa irin wadannan kalamai ba su dace ba kuma suna iya kawo rudani.
Dan majalisar ya jaddada cewa shi ko jam’iyyar APC ba su da wata alaka da lamarin, yana mai kira ga jami’an tsaro su gudanar da cikakken bincike ba tare da son rai ba domin gano hakikanin abin da ya faru.
Sanarwar ta ce wasu bayanan farko daga al’umma sun nuna yiwuwar rikici tsakanin wasu bangarori masu adawa da juna, amma ta kara da cewa bincike ne kawai zai tabbatar da gaskiyar lamarin.
Oke ya bukaci ‘yan siyasa da mazauna yankin da su bai wa jami’an tsaro damar gudanar da aikinsu cikin kwarewa tare da kauce wa kalaman da za su iya tayar da hankali ko kara rura wutar rikici.
Ya kuma yi kira da a mutunta rayuwar dan Adam tare da gujewa amfani da irin wannan lamari na bakin ciki wajen cimma manufofin siyasa.
